Shugaba Donald Trumo, jiya jumma’a, yace Amurka ta kai hari kan duk wani muradun soja a wani tsibirin kasar Iran da ake kira Kharg, wadda babban wurin jigilar kayayyaki zuwa ketare.
“Saboda dottaku, naki na lalata illahirin kayan ayyukan mai dake tsibirin,” Mr. Trump ya rubuta a shafinsa na Truth Social.
Amma idan Iran, ko wani ko wata kasa daban ta dauki mataki na katsalandan ga zirga zirgan jirage a mashigin ruwa na Hormuz, zan sake shawara.”
Sai dai kuma, mun sami labarin cewa, wani hari da Iran ta kai a wani sansanin jiragen sama na soja da ake kira Yerima Sultan dake Saudiyya ya lalata jiragen sama masu karawa jirage mai a sararin sama na Amurka guda biyar, kamar yadda jaridar Wall Street ta wallafa ranar Jumma’a, jaridar ta ambaci majiyoyi guda biyu dangane da wannan labari.
Jiragen da suka lalace sakamakon wani hari da makami mai linzami da Iran ta kai a cikin kwanakin nan, bai lalata su baki daya ba ana nan ana gyara su, kamar yadda Jaridar ta fada, kuma ta kara da cewa babu wanda ya mutu sakamakon harin.
Haka ma a Iraqi, an kaiwa wani jirgin ruwa na dakon mai na Amurka hari ranar laraba a gabar ruwan Iraqi, inda kananan jiragen ruwa da aka dankarawa nakiyoyi suka afkawa jirgin ruwa, nan da nan jirgin ruwa ya kama da wuta, ya zamanto ma’aikatan jirgin basu da isashen lokaci na tserewa, kamar yadda binciken farko da mai jirgin ruwa ya fada.
Jirgin mai suna SafeSea Vishnu mai cibiya a jihar New Jersey na Amurka, masu jirgin a cikin sanarwa da suka bayar suka ce “An kitsa kai harin ne da gangan,” masu jirgin suka fada bayan da suka zanta da ma’aikatan jirgin wadanda suka tsira.


