Shugaban Amurka Donald Trump, yayi gargadi a yau Litinin cewa za’a tarwatsa cibiyoyin makamashi da rijiyoyin mai na kasar Iran idan bata bude mashigin ruwa na Hormuz ba. Wannan ya biyo bayan da Iran ta kira tsarin yarjejeniyar wanzar da zaman lafiya da Amurka ta kafa a matsayin abu ba mai yiwuwa ba, kuma ta kai hare-hare da makamai masu linzami kan kasar Isra’ila.
Sojin Isra’ila sun ce an kado wani jirgi mara matuki na drone da yemen ta harba musu a yau Litinin, kwanaki biyu bayan ‘yan kungiyar Houthi na Yemen sun shiga fadan a bayan Iran, inda suka harba makamai zuwa Isra’ila. Suma kungiyar Hezbollah na Lebanon sun harbawa Isra’ila rokoki.
Ita ma Isra’ila ta kai hare-hare da Makamai masu linzami kan sansanin soji a Tehran da kuma sansanin ‘yan kungiyar Hezbolla a Beirut.
A yau Iran ta tabbatar da kisan kwamandan sojin ruwan ta Alireza Tangsiri, na kwana-kwanan nan cikin jerin manyan mutanen ta da aka kashe tun bayan kashe shugaban kolin ta Ayatollah Ali Khameni a farkkon yakin.


