Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna Afrika
  • Tinubu Ya Buƙaci Musulmi Su Riƙe Haƙuri, Tawali’u Da Tausayi Afrika
  • Maulidin 2026: IMC Ta Yi Kira Da Ƙarfafa Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Najeriya Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai Afrika
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika

Shugaban Ukraine Ya Tattauna Da Trump Akan Zaman Lafiya
Published: December 27, 2025 at 5:48 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 27, 2025

Shugaban kasar Ukrain, Volodymr Zelensky yana so ya tattauna kan batutuwan da suka Shafi yankunan kasar da shugaban Amurka Donald Trump, wadanda su ne manyan abubuwa da suke kawo cikas wajen kawo karshen yakin ta da kasar Rasha.

Shugabannin biyu zasu tattauna ne a jihar Florida ranar Lahadi, a yayin da aka kusa karkare shirin zaman lafiya mai matakai ashirin, da kuma tabbatar da tsaro.

Da yake sanar wa da manema labarai kan batun tattaunawar, Zelensky ya ce za’a iya cimma matsaya da dama kafin zuwan sabuwar shekara, saboda fadar Washington ta zage dantse wajen ganin ta kawo karshen yaki gadan-gadan da Rasha ke yi da Ukrain, wanda ya kasance mafi muni a tarayyar turai tun bayan yakin duniya na biyu.

Israela ta kasance kasa ta farko da ta amince da Jamhuriyar Somaliland, da ta ayyana kan ta a matsayin kasa me cin gashin kan ta, ranar Jumu’a kuma wannan kuduri zai iya sauya fasalin dabi’un yankuna, kuma zai kawo kalubale ga ra’ayin Somalia na rashin son a warewa

Fira minista Benjamin Netanyahu, ya ce Israila zata nemi hadin guiwa da Somaliya a harkar noma, lafiya, fasaha da kuma tattalin arziki kuma a wani jawabi ya taya shugaban Somaliya Abdulrahman Muhammad Abdullahi murna, tare da yaba yadda yake gudanar da mulkin sa, ya kuma gayyace shi ya kai ziyara Israil.

Netanyahu ya ce wannan furuci, na daga cikin tsarin hadakar yankuna na Abraham Accords, wanda aka rattaba hannu a kai bisa ga shawara shugaba Donald Trump.

An kulla yarjejeniyar ne da aka tsara a shekarar 2020, lokacin mulkin Trump na farko, kuma ta kunshi kasar Isra’ila ta yi huldar diplomassiya bisa ka’ida da kasashen hadaddiyar daular larabawa, da Bahrain, tare da wasu kasashen da suka hadu daga baya.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda
Next Post: Najib Razak Zai Kara Shekaru 15 A Gidan Yari Saboda Cin Zarafin Kujerar Mulki

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
An Yi Fashin Kaguwa Da Dodon-Kodi Na Miliyoyin Dalar Amurka Amurka
Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran Afrika
Angano Gawar Wani Dan Myanmar A Arewacin New York Afrika
Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya Amurka
Kakakin Majalisar Kasar Amurka Yana Tsaka Mai Wuya Game Da Kasafin Kudi Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • UEFA Tana Shirin Janye Barazanar Kauracewa Gasar FIFA
  • Feyenoord Ta Fara Tattaunawa Da Manchester United Kan Daukar Chido Obi Aro 
  • Fanny Amun Ya Yi Murabus A Matsayin Shugaban Kwamitin Binciken NFF
  • Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna
  • Tinubu Ya Buƙaci Musulmi Su Riƙe Haƙuri, Tawali’u Da Tausayi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
  • Gwamnatin Filato Ta Gurfanar Da Maharan Rukuba A Kotu Afrika
  • NDPHC Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Gombe Wajen Inganta Wutar Lantarki Afrika
  • Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Nuhu Ribadu Ya Mika Yara 130 Da Aka Kubutar Ga Gwamna Bago Tsaro
  • Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani Najeriya
  • Shugaba Tinubu Zai Kara Karbo Bashin Dala Miliyan 516 Afrika
  • Motsepe, Daga 2028 AFCON Zata Sauya Daga Shekaru Biyu Zuwa Hudu Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.