Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaban Ukraine Ya Tattauna Da Trump Akan Zaman Lafiya
Published: December 27, 2025 at 5:48 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 27, 2025

Shugaban kasar Ukrain, Volodymr Zelensky yana so ya tattauna kan batutuwan da suka Shafi yankunan kasar da shugaban Amurka Donald Trump, wadanda su ne manyan abubuwa da suke kawo cikas wajen kawo karshen yakin ta da kasar Rasha.

Shugabannin biyu zasu tattauna ne a jihar Florida ranar Lahadi, a yayin da aka kusa karkare shirin zaman lafiya mai matakai ashirin, da kuma tabbatar da tsaro.

Da yake sanar wa da manema labarai kan batun tattaunawar, Zelensky ya ce za’a iya cimma matsaya da dama kafin zuwan sabuwar shekara, saboda fadar Washington ta zage dantse wajen ganin ta kawo karshen yaki gadan-gadan da Rasha ke yi da Ukrain, wanda ya kasance mafi muni a tarayyar turai tun bayan yakin duniya na biyu.

Israela ta kasance kasa ta farko da ta amince da Jamhuriyar Somaliland, da ta ayyana kan ta a matsayin kasa me cin gashin kan ta, ranar Jumu’a kuma wannan kuduri zai iya sauya fasalin dabi’un yankuna, kuma zai kawo kalubale ga ra’ayin Somalia na rashin son a warewa

Fira minista Benjamin Netanyahu, ya ce Israila zata nemi hadin guiwa da Somaliya a harkar noma, lafiya, fasaha da kuma tattalin arziki kuma a wani jawabi ya taya shugaban Somaliya Abdulrahman Muhammad Abdullahi murna, tare da yaba yadda yake gudanar da mulkin sa, ya kuma gayyace shi ya kai ziyara Israil.

Netanyahu ya ce wannan furuci, na daga cikin tsarin hadakar yankuna na Abraham Accords, wanda aka rattaba hannu a kai bisa ga shawara shugaba Donald Trump.

An kulla yarjejeniyar ne da aka tsara a shekarar 2020, lokacin mulkin Trump na farko, kuma ta kunshi kasar Isra’ila ta yi huldar diplomassiya bisa ka’ida da kasashen hadaddiyar daular larabawa, da Bahrain, tare da wasu kasashen da suka hadu daga baya.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda
Next Post: Najib Razak Zai Kara Shekaru 15 A Gidan Yari Saboda Cin Zarafin Kujerar Mulki

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’an Shige Da Ficen Amurka Sun Harbe Wani Har Lahira Amurka
Sakataren Harkokin Wajen Amurka Yace Rahoton Kasashe Biyar Akan Rasha Yana Dauke Da Damuwa Amurka
Za’a Saka Tarihin Trump A Manhajar Makarantu Don Jajircewasa Da Kwazo Amurka
Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke Amurka
Shugaba Donald Trump Yabada Umarnin Hana Jiragen Dakon Mai Shiga Venezuela Amurka
Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar Amurka
  • Kungiyar ISIS Ta Dauki Alhakin Harin Kasar Nijar Afrika
  • Lawal, Filin Wasa Na Rashidi Yekini Ko Turai Iyaka Wasanni
  • Za’a Dauko Messi Aro Zuwa Barcelona Deco Wasanni
  • ‘Yan Sandan Habasha Sun Kama Dubban Albarusai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca Wasanni
  • Kungiyar MDD Ta Bukaci Ayi Bincike Game Da Kashe ‘Yan Iran Sauran Duniya
  • Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.