Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • IMC Kaduna Ta Buƙaci Jama’a Su Fifita Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Afrika
  • Gwamna Namadi Ya Amince Da Naɗin Sabon Sarkin Gumel Afrika
  • Hukumar Ruwa Ta Gombe Ta Horas Da Ma’aikatan Sashen Kasuwanci Kan Ka’idojin Aiki Afrika
  • Majalisar Malaman Yarbawa Ta Yi Jimamin Rasuwar Babban Limamin Nuruddeen A Gombe Afrika
  • ‘Yan Sanda Sun Haramta Amfani Da Drones Ba Tare Da Izinin NCAA Ba Afrika

Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna
Published: May 27, 2026 at 6:37 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Muhammadu Inuwa Yahaya ya taya al’ummar Musulmi murnar bikin Eid el-Kabir na bana, inda ya yi kira ga muminai da su rungumi dabi’un sadaukarwa, ƙauna, haɗin kai da biyayya kamar yadda Annabi Ibrahim (AS) ya nuna kuma Annabi Muhammad (SAW) ya tabbatar.

A cikin saƙon taya murna da ya fitar domin bikin Sallah, gwamnan ya bayyana Eid el-Kabir a matsayin lokaci na sadaukarwa, rabon arziki da tausayi, yana mai kira ga Musulmi da su ci gaba da tabbatar da zaman lafiya da zaman tare cikin jituwa a cikin al’umma.

Gwamna Inuwa Yahaya ya jaddada muhimmancin ci gaba da yin addu’o’i domin zaman lafiya, ci gaba da bunƙasar tattalin arziki mai ɗorewa a Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya, musamman duba da ƙalubalen tattalin arziki da matsalolin tsaro da ƙasar ke fuskanta.

“Jihar Gombe na cikin zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba, kuma hakan ya samo asali ne daga ruhin zaman lafiya, haɗin kai duk da bambance-bambance da kuma haƙuri da aka daɗe ana gina wa a tsakanin al’ummarmu. Don haka ina kira gare mu da mu ci gaba da kiyaye wannan kyakkyawan yanayi,” in ji gwamnan.

Gwamnan, wanda kuma shi ne shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, ya bayyana cewa bikin Eid na bana ya zo ne daidai da fara harkokin siyasa gabanin babban zaɓen shekarar 2027, inda ya yi gargadin kada siyasa ta mamaye darussa da muhimmancin ibadar da ke cikin wannan biki.

A cewarsa, wannan lokaci ya kamata ya zama tunatarwa kan tausayi, sadaukarwa, biyayya ga Allah Maɗaukakin Sarki da kuma ƙaunar juna, maimakon rarrabuwar kai da gasa ta siyasa mara kyau.

Ya kuma bayyana godiyarsa ga sarakunan gargajiya, shugabannin addini da na al’umma, tare da daukacin jama’ar Jihar Gombe bisa ci gaba da ba gwamnatinsa haɗin kai da goyon baya.

Gwamnan ya sake jaddada ƙudirin gwamnatinsa na ci gaba da aiwatar da manufofi, shirye-shirye da ayyukan ci gaba da za su bunƙasa tattalin arziki da rayuwar al’ummar jihar.

Haka kuma, ya buƙaci mazauna jihar da su kasance masu lura da tsaro tare da kai rahoton duk wani abu da ake zargi da zai iya barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankalin da ake morewa a jihar.

“Gwamnati ba za ta yi watsi da babban nauyin da ke kanta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a ba. Za mu ci gaba da tallafawa jami’an tsaro domin tabbatar da dorewar zaman lafiya da tsaro a faɗin jiharmu,” in ji shi.

Dangane da damina kuwa, Gwamna Inuwa Yahaya ya yi kira ga jama’a da su yi addu’ar samun wadataccen ruwan sama da albarkar noma, tare da ɗaukar matakan kariya daga ambaliya.

Ya shawarci jama’a da su tsaftace muhallansu, su buɗe magudanan ruwa tare da kauce wa zama a wuraren da ambaliya ke yawan faruwa domin rage illolin ambaliyar ruwa a lokacin damina.

A ƙarshe, gwamnan ya yi addu’ar Allah Ya sa a gudanar da bikin Eid cikin zaman lafiya, kwanciyar hankali da albarkar Allah ga al’ummar Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP
Next Post: Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai

Karin Labarai Masu Alaka

An Yankewa Prime Ministan Kasar Tunisiya Hukuncin Shekaru 24 A Gidan Yari Afrika
Jirgin Sojojin Ruwa Yayi Gobara A Cross River Najeriya
Gwamnatin Trump Tana Cigaba Da Korar Baki Daga Amurka Afrika
Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Thailand Da Cambodia Sun Fara Tattauunawa Kan Batun Tsagaita Wuta Labarai
An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • IMC Kaduna Ta Buƙaci Jama’a Su Fifita Haɗin Kai Da Zaman Lafiya
  • Gwamna Namadi Ya Amince Da Naɗin Sabon Sarkin Gumel
  • Hukumar Ruwa Ta Gombe Ta Horas Da Ma’aikatan Sashen Kasuwanci Kan Ka’idojin Aiki
  • Majalisar Malaman Yarbawa Ta Yi Jimamin Rasuwar Babban Limamin Nuruddeen A Gombe
  • ‘Yan Sanda Sun Haramta Amfani Da Drones Ba Tare Da Izinin NCAA Ba

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa Afrika
  • Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
  • Sanata Goje: Sakamakon Zaben Daga Abuja Zai Fito Afrika
  • Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa Afrika
  • Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa Wasanni
  • Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.