Shugaban kasar Ivory coast Allassane Ouattara yayi garambawul ga majalisar ministocin kasar, inda ya daukaka kani ko dan’uwansa wanda shine ministan tsaro, yanzu ya sami karin mukami na zama mukaddashin PM kasar. Tene Birahima Ouattara, zai kuma ci gaba da rike mukaminsa na ministan tsaro.
Wannan mataki ya kara daukaka kanin na sa kan madafun iko, yayinda sauran ministoci kowa yana daram kan kujerarsa.
Garambawul din nan ya biyo bayan nasarar sake cin zabe da shugaba Ouattara yayi cikin watan Oktoba, da kuma nasarar jam’iyyarsa na samun rinjaye a zaben majalisar dokokin kasar da aka yi cikin watan Disamba bara.
Shugaba Ouattara dan shekaru 84 da haifuwa, wanda tsohon mataimakin darektan asusun bada lamuni na duniya da aka fi sani da lakabin IMF, yana jan ragamar kasarsa tun a shekara ta 2011, yace yana so ya share fage ga sabbin jini da za su shugabanci kasar tun yana kan mulki.
Wadan nan sauye sauye suna zuwa ne a lokacin da Ivory Coast, kasar da Allah Ya yiwa albarkar Cocoa fiye da ko wace kasa a duniya ta kokarin ta kara zugu kan ci gaban tattalin arziki na tsawon shekaru 15, wadda yasa kasar ta zama wacce tattalin arzikinta yafi bunkasa a yankin baki daya.


