Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili
Published: December 5, 2025 at 7:27 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 5, 2025

Rundunar sojojin Amurka ta ce ta kai hari a kan wani karamin jirgin ruwan da ake zargin na safarar muggan kwayoyi ne a yankin ruwa na kasa da kasa a gabashin tekun Pacific jiya alhamis, ta kashe mutane hudu.

Rundunar sojojin ta Amurka, ta fada cikinwata sanarwar da ta bayar a dandalin sada zumunta na X cewa bayanan leken asiri sun tabbatar da cewa jirgin ruwan yana dauke da muggan kwayoyi, kuma an kai masa hari a kan hanyar da masu safarar muggan kwayoyi suka saba bi a gabashin tekun Pacific.

A halin da ake ciki, ‘yan majalisar dokokin Amurka sun samu ganin takardar dake kunshe da takaitaccen bayani da ya tsara matakan da gwamnatin Trump take dauka na kai hari kan jiragen ruwan da ake zargin suna dauke da kwayoyi a tekun Pacific.

‘Yan majalisar suna daukar wannan takarda a zaman mai muhimmanci ga binciken da suke yi na wani harin da sojojin Amurka suka kai kan wani jirgin a ranar 2 ga watan Satumba, inda suka kashe mutane 11, cikinsu har da wasu mutane biyu da suka kubuta da rai daga harin farko da aka kai kan jirgin.

Wannan takardar da ta takaita bayanin tana dauke da shafuka biyu, kuma ta zayyana jerin masu bayarda umurni, da yadda gwamnatin Trump take amfani da bnayanan leken asiri wajen gano irin wadannan jirage.

‘Yan majalisar sun bukaci da a kawo musu cikakkiyar takardar wadda ke dauke da bayanin komai da komai game da hare-haren, amma ba a san ko ma’aikatar tsaro zata yarda su gani ba.

A halin da ake ciki dai, manyan ‘yan jam’iyyar Democrat a majalisar dokoki dake cikin wadanda aka yi ma bayanin wasu hare-haren da aka kai a tekun Caribbean sun fada jiya alhamis cewa hankulansu sun tashi da bidiyon da suka gani na wasu mutane biyu da suka kubuta da rai, amma sai aka kara kai musu hari aka kashe su, Sai dai kuma takwarorinsu na Republican sun kare wannan hari na biyu da cewa bai saba ma doka ba.

Babban dan jam’iyyar Democrat a kwamitin kula da ayyukan leken asiri a majalisar wakilai, Jim Himes yace sun ga mutane biyu wadanda ba su da wata hanyar da zasu iya zuwa wani wuri, da jirginsu da aka gama lalatawa, amma sai aka kashe su.

Yace wannan abu na daya daga cikin abubuwa mafi tashin hankali da ya gani.

Shi ma babban dan Demicrat a kwamitin kula da ayyukan soja na majalisar dattijai, Jack Reed, yace hankalinsa ya tashi matuka da wannan bidiyo da ya gani kuma ya kamata a sake shi jama’a su gani.

Amma kuma shugaban kwamitin ayyukan leken asiri na majalisar dattijai dan jam’iyyar Republican, Tom Cotton, cewa yayi shi abinda ya gani mutanen biyu suna kokarin su juya jirginsu da ya kife ne, dauke da muggan kwayoyi zuwa Amurka domin su ci gaba da fafatawa.

Amurka

Post navigation

Previous Post: CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya
Next Post: Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Kasuwannin Hannayen Jari Suna Fuskantar Durkushewa Sakamakon Matsin Lambar Shugaba Trump Amurka
Shugaba Trump Yayi Barazanar Tura Sojoji Ga Masu Zanga Zanga Amurka
Shugaban Amurka Donald Trump Ya Jadda da Kudirinsa Da Kwace Iyakar Greenland Amurka
Ansamu Maganin Da Yake Rage Kitsen Jijiyoyi A Amurka Amurka
Kasar Amurka Takara Saka Takunkumi Akan Kasar Venezuela Amurka
Kasar Rasha Ta Zargi Ukraine Da Kai Hari Gidan Shugaban Rasha Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Majalisar Dattawa Ta Wanke Janar Christopher Musa A Matsayin Minista Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar Labarai
  • Bana Ba Harka Ga ‘Yan-Wasan Kwallon Kafar Najeriya Wasanni
  • Kungiyar Maharba Da ‘Yan Sintiri Sun Samu Kyautar Motoci Labarai
  • Anfara Kirga Kuri’a A zaben Kasar Guinea Labarai
  • ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
  • Lawal, Filin Wasa Na Rashidi Yekini Ko Turai Iyaka Wasanni
  • China Ta Dawo Da Harajin Magungunan Hana Haihuwa Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.