Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya
Published: December 18, 2025 at 3:32 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Ganin yadda rabuwar kawunan al-uma da banbance banbance awarewacin Najeriya ke kara rura wutar matsalar tsaro ya sa kungiyoyin yankin hada wata sabuwar kungiyar sulhu da sasanta juna domin hada kan al-umar yankin da nufin magance matsalolin tsaro da tattalin arziki da riki tsakin al-umomin yankin baki daya.
Sabuwar kungiyar sulhu da hada kawunan al-uma a arewacin Najeriyan da ke karkashin Jagorancin tsohon mai-baiwa shugaban kasa shawara kan ta harkokin siyasa a offishin mataimakin shugaban kasa Dr. Hakeem Baba-Ahmed ta hada da kungiyar musulmin Najeriya ta Jama’atu Nasrul-Islam da kuma ta Kiristoci CAN da sauran kungiyoyin arewa kuma a jiya Laraba kungiyar ta fara ziyarar hada kawunan al-umar yankin baki daya.
Daga Kaduna, Wakilin mu Isah Lawal Ikara ya bi tawagar kungiyar zuwa ofisoshin kungiyar Jama’atu Nasrul-Islam da kuma Kungiyar Kiristocin Najeriya ta CAN, kuma ga rahoton da ya aiko mana……
Rashin jituwa tsakanin mabiya addinin Musulunci da Kirista da kuma maganar matsalar tsaro da talauci dai na cikin manyan matsalolin dake damun yankin arewacin Najeriya, harma wasu na ganin hakan ne ya sa shugaba Donald Trump na Amurka barazar aike sojoji yankin da sunan yakar  ‘yan-ta’adda. Sai dai shugaban wannan kungiya ta sulhu Dr. Hakeem Baba-Ahmed ya ce kungiyar ta shirya share  wannan damuwa dake damun Arewa.
Shugaban kungiyar Kiristocin Najeriya reshen  Arewaci Rebaren Joseph John Hayaf ya ce gaske an sami baraka tsakanin al-umar arewa a baya amma yanzu an gano bakin zaren.
Babban Sakataren kungiyar Jama’atu Nasrul-Islam na Kasa Farfesa Khalid Aliyu Abubakar ya ce Arewa ta gane ciwon da ke damun ta kuma ta samu magani.
Game da banbancin wannan sabuwar kungiyar sulhu da sauran kungiyoyin da aka kafa da irin wadan nan manofofi a arewa kuwa, Rebaren Joseph John Hayaf ya ce ita wannan sabuwar kungiyar hadaka ce ta dukkan manyan kungiyoyin arewacin Najeriya.
Arewacin Najeriya dai ya sha fara da rikice-rikicen addini da na kabilanci wanda wasu ke ganin matsalar tsaron dake damun yankin ma ana shafa mata addini da kabilanci duk lolacin da ‘yan-ta’adda ko ‘yan-bindiga su ka kashe mutane. Abun jira a gani kuma shine, shin wannan sabuwar kungiyar za ta iya magance wannan matsalar da ta ki-ci ta-ki cinyewa.
Labarai

Post navigation

Previous Post: Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba
Next Post: Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC

Karin Labarai Masu Alaka

Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak Labarai
Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai
Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu Afrika
‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
An Sako Dan Siyasar Kasar Venezuela Daga Gidan Yari Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani Najeriya
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya Wasanni
  • An Katse Intanet Da Wayar Tarho A Kasar Uganda Siyasa
  • Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
  • Venezuela Ta Sako Karin Mutanen Da Take Tsare Dasu Labarai
  • Kasar Amurka Da Denmark Suna Rikici Akan Iyakar Greenland Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.