Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya
Published: December 18, 2025 at 3:32 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Ganin yadda rabuwar kawunan al-uma da banbance banbance awarewacin Najeriya ke kara rura wutar matsalar tsaro ya sa kungiyoyin yankin hada wata sabuwar kungiyar sulhu da sasanta juna domin hada kan al-umar yankin da nufin magance matsalolin tsaro da tattalin arziki da riki tsakin al-umomin yankin baki daya.
Sabuwar kungiyar sulhu da hada kawunan al-uma a arewacin Najeriyan da ke karkashin Jagorancin tsohon mai-baiwa shugaban kasa shawara kan ta harkokin siyasa a offishin mataimakin shugaban kasa Dr. Hakeem Baba-Ahmed ta hada da kungiyar musulmin Najeriya ta Jama’atu Nasrul-Islam da kuma ta Kiristoci CAN da sauran kungiyoyin arewa kuma a jiya Laraba kungiyar ta fara ziyarar hada kawunan al-umar yankin baki daya.
Daga Kaduna, Wakilin mu Isah Lawal Ikara ya bi tawagar kungiyar zuwa ofisoshin kungiyar Jama’atu Nasrul-Islam da kuma Kungiyar Kiristocin Najeriya ta CAN, kuma ga rahoton da ya aiko mana……
Rashin jituwa tsakanin mabiya addinin Musulunci da Kirista da kuma maganar matsalar tsaro da talauci dai na cikin manyan matsalolin dake damun yankin arewacin Najeriya, harma wasu na ganin hakan ne ya sa shugaba Donald Trump na Amurka barazar aike sojoji yankin da sunan yakar  ‘yan-ta’adda. Sai dai shugaban wannan kungiya ta sulhu Dr. Hakeem Baba-Ahmed ya ce kungiyar ta shirya share  wannan damuwa dake damun Arewa.
Shugaban kungiyar Kiristocin Najeriya reshen  Arewaci Rebaren Joseph John Hayaf ya ce gaske an sami baraka tsakanin al-umar arewa a baya amma yanzu an gano bakin zaren.
Babban Sakataren kungiyar Jama’atu Nasrul-Islam na Kasa Farfesa Khalid Aliyu Abubakar ya ce Arewa ta gane ciwon da ke damun ta kuma ta samu magani.
Game da banbancin wannan sabuwar kungiyar sulhu da sauran kungiyoyin da aka kafa da irin wadan nan manofofi a arewa kuwa, Rebaren Joseph John Hayaf ya ce ita wannan sabuwar kungiyar hadaka ce ta dukkan manyan kungiyoyin arewacin Najeriya.
Arewacin Najeriya dai ya sha fara da rikice-rikicen addini da na kabilanci wanda wasu ke ganin matsalar tsaron dake damun yankin ma ana shafa mata addini da kabilanci duk lolacin da ‘yan-ta’adda ko ‘yan-bindiga su ka kashe mutane. Abun jira a gani kuma shine, shin wannan sabuwar kungiyar za ta iya magance wannan matsalar da ta ki-ci ta-ki cinyewa.
Labarai

Post navigation

Previous Post: Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba
Next Post: Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC

Karin Labarai Masu Alaka

Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato Labarai
Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
Gwamna Ahmad Aliyu Na Jihar Sokoto Ya Gabatar Da Kasafin Fiye Da Naira Biliyan 700 Labarai
Hukumar NAPTIP Ta Kubutar Da Yara 11 Daga Hannun Masu Safara Mutane Labarai
Za A Rantsar Da Mainasara Kogo A Matsayin Shugaban Kundin Da’ar Ma’aikata Labarai
Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC
  • Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba
  • Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC
  • FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u Siyasa
  • Onana Ba Ya Cikin Tawagar Kamaru (AFCON) Wasanni
  • Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu Afrika
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Anyi Jefe-Jefe Yayin Rangadin Messi, A Indiya Wasanni
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Roger Lumbala Shekaru 30 Labarai
  • An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.