Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya
Published: December 18, 2025 at 3:32 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Ganin yadda rabuwar kawunan al-uma da banbance banbance awarewacin Najeriya ke kara rura wutar matsalar tsaro ya sa kungiyoyin yankin hada wata sabuwar kungiyar sulhu da sasanta juna domin hada kan al-umar yankin da nufin magance matsalolin tsaro da tattalin arziki da riki tsakin al-umomin yankin baki daya.
Sabuwar kungiyar sulhu da hada kawunan al-uma a arewacin Najeriyan da ke karkashin Jagorancin tsohon mai-baiwa shugaban kasa shawara kan ta harkokin siyasa a offishin mataimakin shugaban kasa Dr. Hakeem Baba-Ahmed ta hada da kungiyar musulmin Najeriya ta Jama’atu Nasrul-Islam da kuma ta Kiristoci CAN da sauran kungiyoyin arewa kuma a jiya Laraba kungiyar ta fara ziyarar hada kawunan al-umar yankin baki daya.
Daga Kaduna, Wakilin mu Isah Lawal Ikara ya bi tawagar kungiyar zuwa ofisoshin kungiyar Jama’atu Nasrul-Islam da kuma Kungiyar Kiristocin Najeriya ta CAN, kuma ga rahoton da ya aiko mana……
Rashin jituwa tsakanin mabiya addinin Musulunci da Kirista da kuma maganar matsalar tsaro da talauci dai na cikin manyan matsalolin dake damun yankin arewacin Najeriya, harma wasu na ganin hakan ne ya sa shugaba Donald Trump na Amurka barazar aike sojoji yankin da sunan yakar  ‘yan-ta’adda. Sai dai shugaban wannan kungiya ta sulhu Dr. Hakeem Baba-Ahmed ya ce kungiyar ta shirya share  wannan damuwa dake damun Arewa.
Shugaban kungiyar Kiristocin Najeriya reshen  Arewaci Rebaren Joseph John Hayaf ya ce gaske an sami baraka tsakanin al-umar arewa a baya amma yanzu an gano bakin zaren.
Babban Sakataren kungiyar Jama’atu Nasrul-Islam na Kasa Farfesa Khalid Aliyu Abubakar ya ce Arewa ta gane ciwon da ke damun ta kuma ta samu magani.
Game da banbancin wannan sabuwar kungiyar sulhu da sauran kungiyoyin da aka kafa da irin wadan nan manofofi a arewa kuwa, Rebaren Joseph John Hayaf ya ce ita wannan sabuwar kungiyar hadaka ce ta dukkan manyan kungiyoyin arewacin Najeriya.
Arewacin Najeriya dai ya sha fara da rikice-rikicen addini da na kabilanci wanda wasu ke ganin matsalar tsaron dake damun yankin ma ana shafa mata addini da kabilanci duk lolacin da ‘yan-ta’adda ko ‘yan-bindiga su ka kashe mutane. Abun jira a gani kuma shine, shin wannan sabuwar kungiyar za ta iya magance wannan matsalar da ta ki-ci ta-ki cinyewa.
Labarai

Post navigation

Previous Post: Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba
Next Post: Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC

Karin Labarai Masu Alaka

Ruwa Kamar Da Bakin Kwarya Ya Haifar Da Mutuwar Mutane A Nairobi Afrika
Jam’iyyar APC Ta Rantsar Da Sabbin Shugabanni a Jihar Neja Labarai
Hukumomin Kasar China Suna Goyon Bayan Somaliya Labarai
Kudin Man Fetur Ya Karu Da Kashi 10 Cikin 100 Afrika
Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika
Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Gaddafi A Gidansa Dake Kasar Libya Afrika
  • Jirgi Marar Matuka Yayi Luguden Wutan A Abu Dhabi Afrika
  • An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugabar Kungiyar Cinikayya Ta Duniya Ta Bukaci Kasashe Su Gyara Harkokin Cinikayya Afrika
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
  • An Kama Masu Fasa Kaurin Gawayi A Malawi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.