Wasu ‘yan asalin kasar Venezuela da suka yi kaura suka bazu kasashen da ke yankin kudancin Amurka, sun fara tunanin ko su koma gida tun bayan hambarar da shugaba Nicolas Maduro daga mulki, inda suke fatan za’a gabatar da zaben sabuwar gwamnati bisa tsarin demokradiya wadda zata magance rugujewar tattalin arzikin kasar.
A kalla Kashi 25 cikin dari na ‘yan kasar Venezuela sun yi kaura zuwa kasashen dake yankin kudanci Amurka, Caribbean, Spain da kuma kasar Amurka tun shekarar 2014, inda suka gujewa rushewar tattalin arzikin kasar da ta dogara da man fetur, sakamon rikon sakaina daga gwamnati.
Wani likita Juan Carlos Viloria, da ke zaune a kasar Colombia, kasar da ke dauke da mafi Yawan ‘yan gudun hijira daga Venezuela, ya ce ya na so, ya koma kasar sa, domin bada gudummawar sa wajen farfado da ita.
Amma kuma ci gaba da rike ragamar mulki da matamakiyar Nicolas Maduro, Delcy Rodriguez ke yi gam, da jin tsoron samun ci gaba da danniya daga gwamnati, da gurbacewar tattalin arziki, na sa mutane tsoron komawa. Ya kara da cewa mazauna arewa maso gabashin Colombia da yake aiki da su, sun lura akwai karin mutanen dake ratsowa cikin kasar daga Venezuela suyi aiki don su samu kudi, kafin abubuwa suyi sauki a Venezuela.


