Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta
Published: December 13, 2025 at 9:30 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 13, 2025

Cambvodia ta ce sojoji da jiragen yakin kasar thailand suna ci gaba da kai hare-hare a wasu yankunan bakin iyakarsu a ranar asabar da safe, sa’o’i bayan da shugaba Donald Trump na Amurka yayi ikirarin cewa ya kulla yarjejeniyar tsagaita wuta a tsakanin makwabtan biyu.

Ma’aikatar yada labarai ta Cambodia ta ce sojojin Thailand ba su daina kai hare-haren kan cibiyoyin Cambodia ba.

Rundunar sojojin Thailand ta mayarda martani da cewa Cambodia tana ci gaba da keta dokoki na kasa da kasa ta hanyar auna hare-hare a kan cibiyoyin fararen hula tare da dasa nakiyoyi.

Shugaba Trump yace Thailand da Cambodia sun yarda zasu tsagaita bude wuta daga jiya jumma’a a bayan tattaunawar da yayi ta wayar tarho da firayim ministan Thailand Anutuin Charnvirakul da firimiyan Cambodia Hun Manet.

Sai dai kuma babu daya daga cikinsu da yayi maganar cewa an cimma wata yarjejeniya a bayanan da suka yi bayan tattaunawa da shugaban na Amurka, har ma firayim ministan Thailand din yace babu wata tsagaita wutar da aka cimma.

A cikin wata sanarwar da ya fitar ranar asabar a shafin Facebook, firimiyan Cambodia Manet yayi nuni da wayar da suka yi da shugaba trump da tattaunawar da suka yi tun da fari da firayim ministan Malaysia Anwar Ibrahim, yana mai fadin cewa kasarsa tana ci gaba da neman hanyar warware rikicin bakin iyakar cikin lumana.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko
Next Post: Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’in Diflomasiyyar Da Ake Zargi Da Kisan Prime minister Ya Daukaka Kara Afrika
Rundunar Sojin Amurka Sunfara Ficewa Daga Kasar Sham Amurka
Gwamnatin Kano Zata Dauki Mataki Game Da Kisan Dorayi Tsaro
Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
Isra’ila Zata Mamaye Lebanon Labarai
Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • Kamfanin NNPC Yana Tattaunawa Da Wani Kamfanin Kasar China Labarai
  • Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar Amurka
  • Bankin Duniya Zaibawa Kasar Mozambique Lamunin Dala Bilyan Shida Labarai
  • Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Amurka Zai Sake Gine Gaza Amurka
  • Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan Afrika
  • Gwamnatin Somaliya Da MDD Sun Bayyana Cewa Kimanin Mutane Miliyan Shida Da Rabi Suna Fuskantar Barazanar Yunwa Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.