Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC
Published: December 18, 2025 at 9:50 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 18, 2025

Ɗan takarar gwamnan jihar Gombe na jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Muhammad Jibrin Barde, ya fice daga PDP zuwa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) gabanin zaɓen 2027.

Dan Barde ya bayyana hakan a daren ranar Talata a gidansa, inda ya nuna katin zamowa mamba na ADC, yana mai cewa ya dawo ne domin sabunta rajistar sa da jama’rsa

Ya ce ya bar PDP tun farkon shekarar 2025, yana jaddada cewa burinsa shi ne ceto jihar Gombe daga abin da ya bayyana a matsayin mulkin masu harkar kasuwanci.

“Ina tabbatar muku da cewa, kamar yadda kuka sani, ana samun gagarumar tafiya a faɗin ƙasar nan, wadda muka ba wa suna ‘Salon Tafiya’.

“Muna aiki a kan wannan tafiya tare da shugabanninmu a faɗin ƙasar, ciki har da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, tsofaffin gwamnoni da ministoci.

“Manufar wannan tafiya ita ce ceto ƙasar nan daga halin da take ciki na rashin tsaro, matsin tattalin arziki da ƙarancin ababen more rayuwa,” in ji shi.

Jibrin Dan Barde ya ƙara da cewa, “Yana da muhimmanci mu dawo gida domin sabunta rajistar membobimmu kuma mun kuduri aniyar ci gaba da wannan tafiya, kuma yanzu ne lokacin da ya dace mu sake sabunta membobimmu.”

Dangane da haɗin kai, ya ce hadakar ta himmatu matuƙa wajen ceto jihar, yana nuna damuwa kan lalacewar ababen more rayuwa da kuma ƙaruwar rashin tsaro.

“Kamar yadda kuke gani, akwai ƙarancin ababen more rayuwa da kuma rashin tsaro, sannan wannan shine iri rashin ɗaukar alhaki ne muke son yaƙi a jihar nan.

“Muna son samar da shugabanci mai ma’ana, mu bai wa kowa damar cin nasara, mu inganta ilimi ba ilimin da mutum ɗaya ko ƙungiya ke sarrafawa kamar kamfani mai iyaka ba,” in ji shi.

Da yake bayyana dalilin komawa ADC, Dan Barde ya ce jam’iyyar na wakiltar sabon zamani, tare da kira ga wasu da su shigo cikinta.

“Abin da muke son yi yanzu shi ne sabunta membobimmu a ƙarƙashin sabon zamani, kuma ga waɗanda ba mambobi ba, muna kiran su da su shigo ADC domin mu tunkari wannan gwamnati mai ɗaukar alhaki,” in ji shi.

Haka kuma ya gargaɗi al’umma da kada su sayar da ƙuri’un su.

“Kada ku karɓi taliya ko Naira 500 ku sayar da ƙuri’unku yace waɗannan darussa ne masu muhimmanci da ya kamata mu koya

Siyasa

Post navigation

Previous Post: FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca
Next Post: Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Jihar Kano Ya Fice Daga Jam’iyar NNPP Siyasa
‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano Afrika
Malaman Tsangaya A Gombe Sun Goyi Bayan Inuwa Yahaya Da Jamilu Gwamna Afrika
Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
Shugaban Kasar Koriya Ta Arewa Ya Zamo Sakataren Jam’iya Mai Mulki Labarai
Shugaban Kasar Ghana Ya Soki Manufofin Gwamnatin Amurka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • NUJ: Akwai Bukatar Samar Da Inshorar Lafiya Ga ‘Yan Jarida A Najeriya Rediyo
  • Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak Labarai
  • Anyi Sallar Rokon Ruwa A Saudiya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Dakarun Gwamnatin Kasar Sham Tayi Mamaya Zuwa Gabashin Kasar Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tinubu Ta Warware Basussukan Fansho Na Shekaru 18 Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • Guinea An Zabi Madugun Sojojin Da Suka yi Juyin Mulki Mamady A Shugaban Ƙasar, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.