Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka

Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno
Published: December 18, 2025 at 9:00 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mayakan Boko Haram sun sace sabon mataimakin shugaban karamar hukuma da kansiloli a jihar Borno dake arewacin Najeriya

Wasu da ake zargin mambobin kungiyar Boko Haram ne sun sace sabon Mataimakin Shugaban Karamar Hukumar Biu da wasu kansiloli biyu, a kan hanyar Kamuya Buni Yadi, a Jihar Borno.

Majiyoyi da ke kusa da iyalansu sun bayyana sunan Mataimakin Shugaban a matsayin Alhaji Saidu. Kansilolin biyu masu wakiltar mazabun Zarawuyaku da Miringa.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa an zaɓi wadanda aka sace ne kwanaki biyar da suka gabata, a zaben kananan hukumomi da aka gudanar ranar Asabar da ta wuce.

Daya daga cikin majiyoyin ya bayyana cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Laraba, kuma ya shafi wasu matafiya da ke cikin wata motar Hizbah Hummer.

“Gaskiya ne, Alhaji Saidu da kansilolin biyu an sace su ne da hannun wadanda ake zargin ‘yan Boko Haram/ISWAP ne, a tsakanin kauyen Kamuya da hanyar Buni Yadi.

“An sace su tare da wasu fasinjoji da ba a tantance su ba, wadanda ke tafiya cikin wata motar Hizbah daga garin Potiskum na Jihar Yobe zuwa Biu.

“Daya daga cikin kansilolin da aka sace shi ne tsohon Mataimakin Shugaban Karamar Hukumar Biu na nan kusa kuma muna rokon gwamnati da hukumomin tsaro su kara kaimi wajen ceto su da sauran wadanda aka kama” in ji shi.

Kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sanda ta Jihar Borno, ASP Nahum Kenneth Daso, bai yi nasara ba, domin ba a samu damar tuntubarsa ta waya ba, haka kuma bai amsa sakonnin da aka aike masa ba.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela
Next Post: Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati

Karin Labarai Masu Alaka

Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani Afrika
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
Harin Jirgi Maras Matuki Ya Hallaka Mutane A Sudan Labarai
Ankara Gano Wani Abu Mai Kama Da Abun Fashewa A Jabo Jihar Sokoto Tsaro
Gwamnatin Jihar Gombe Ta Haramta Sana’ar Bola Jari Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Hukumar ICPC Ta Gayyaci Dangote Labarai
  • Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai
  • Tsarin Haraji Mai Cike Da Ayoyin Tambaya Na Shirin Fara Aiki Labarai
  • Shin Ko Ganawar Zelensky Da Macron Zata Haifar Da ‘Da Mai Ido? Labarai
  • Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
  • Rikici Tsakanin NNPC Da Kungiyar Gwamnoni Akan Gibin Kudade Labarai
  • Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
  • A Hudubar Kirsimeti Paparoma Leo Ya Jajantawa Al’ummar Falatsinu A Yankin Zirin Gaza Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.