Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Jihar Borno Ce Tayi Nasara A Gasan Karatun Al Qur’ani Na Kasa
Published: December 20, 2025 at 12:44 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jihar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya ce ta lashe matsayi na ɗaya a rukunin maza a Gasar Karatun Al-Qur’ani ta Ƙasa ta shekarar 2025, wadda aka gudanar a Maiduguri ƙarƙashin taken “Borno 2025.”

Wannan gasa ta zama abin tarihi, domin ita ce karo na 40 da ake gudanarwa a Najeriya kuma Borno ta yi nasarar karɓar baƙuncinta cikin nasara.

Yayin sanar da sakamakon gasar, Daraktan Cibiyar Nazarin addinin Musulunci ta Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato, Farfesa Abubakar Yelwa, ya bayyana Musa Ahmed Musa daga jihar Borno a matsayin zakaran a rukunin maza.

A rukunin mata kuma, Hafsat Muhammad Sada daga Jihar Kano ce ta zama Dawisu.

Gasar wadda ta ɗauki tsawon mako guda, ta samu mahalarta mutane 296 daga jihohi 30 na Najeriya, inda suka fafata a rukunai daban daban.

Da yake jawabi a bikin rufe gasar, Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana nasarar gudanar da gasar a matsayin alamar dawowar zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Borno.

Ya ce gasar ta nuna jajircewar al’ummar jihar wajen zaman lafiya, ilimi da koyarwar Musulunci.

“Nasarar ku ba kawai cin gasa ba ce,” in ji Gwamna Zulum ga waɗanda suka yi nasara, “amma wata babbar nasara ce da ta samo asali daga dogon lokaci na jajircewa, himma da girmama Kalmar Allah.”

Ya kuma yaba wa dukkan mahalarta gasar, inda ya ce, “Hakikanin ruhin wannan gasa ba wai lambobin yabo kawai ba ne, amma neman ilimi da jarumtar shiga gasar.”

Gwamnan ya nuna godiya ga Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, da matarsa Hajiya Nana Kashim Shettima, da sauran manyan baƙi da suka bayar da gudunmawa wajen samun nasarar gasar.

Haka kuma, ya yaba da rawar da sarakunan gargajiya, shugabannin jami’o’i, malaman addinai da shugabannin siyasa suka taka wajen nasarar taron.

Manyan baƙi da suka halarci taron sun haɗa da matar Mataimakin Shugaban Ƙasa, Hajiya Nana Kashim Shettima, Gwamnan jihar Katsina, Alhaji Dikko Umar Radda, Mataimakin Gwamnan Jihar Sakkwato, Shehun Borno, Alhaji Abubakar Ibn Umar Garbai El-Kanemi, ‘yan Majalisun Tarayya da jihohi da malaman addini.

Babban abin da ya kayatar a bikin shi ne rabon kyaututtuka da lambobin yabo ga waɗanda suka yi nasara, wanda matar Mataimakin Shugaban Ƙasa ta gabatar.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi
Next Post: Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Zuwa Jami’ar Sheikh Dahiru Bauchi

Karin Labarai Masu Alaka

Kwamitin Ardo Chindo Ya Buƙaci A Hana Mamaye Filayen Kiwo da Gandun Daji Afrika
Man Da Matatar Dangote Take Fitarwa Zuwa Kasashen Afirka Ya Karu Afrika
’Yan Sanda, Sojoji Da DSS Sun Ceto ‘Yan NYSC Da Aka Sace A Kogi Afrika
Kungiyar Cigaban Al’ummar Tangale Tace Bata Goyon Bayan Kai Ziyara Wa Gwamnan Gombe Labarai
Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kuɗin 2026 Najeriya
Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tattalin Arzikin Kasar Congo Ya Bunkasa Labarai
  • Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika
  • Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Tabbas Za’a Gudanar Da Gasar Firimiya Lig Ta Najeriya Wasanni
  • An Binne Gawar Tsohon Shugaban Sashen Hausa Na VOA, Leo Keyen Afrika
  • Borno: An Yi Kwanton Bauna Kan Ayarin Ɗan Takarar Gwamna Afrika
  • Pakistan Da Afghanistan Sun Shiga Kwana Na Biyar Suna Fafatawa Afrika
  • Harin Makami Mai Linzami Da Rasha Ta Kai Yayi Barna Sosai A Ukraine Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.