Jihar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya ce ta lashe matsayi na ɗaya a rukunin maza a Gasar Karatun Al-Qur’ani ta Ƙasa ta shekarar 2025, wadda aka gudanar a Maiduguri ƙarƙashin taken “Borno 2025.”
Wannan gasa ta zama abin tarihi, domin ita ce karo na 40 da ake gudanarwa a Najeriya kuma Borno ta yi nasarar karɓar baƙuncinta cikin nasara.

Yayin sanar da sakamakon gasar, Daraktan Cibiyar Nazarin addinin Musulunci ta Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato, Farfesa Abubakar Yelwa, ya bayyana Musa Ahmed Musa daga jihar Borno a matsayin zakaran a rukunin maza.
A rukunin mata kuma, Hafsat Muhammad Sada daga Jihar Kano ce ta zama Dawisu.
Gasar wadda ta ɗauki tsawon mako guda, ta samu mahalarta mutane 296 daga jihohi 30 na Najeriya, inda suka fafata a rukunai daban daban.
Da yake jawabi a bikin rufe gasar, Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana nasarar gudanar da gasar a matsayin alamar dawowar zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Borno.

Ya ce gasar ta nuna jajircewar al’ummar jihar wajen zaman lafiya, ilimi da koyarwar Musulunci.
“Nasarar ku ba kawai cin gasa ba ce,” in ji Gwamna Zulum ga waɗanda suka yi nasara, “amma wata babbar nasara ce da ta samo asali daga dogon lokaci na jajircewa, himma da girmama Kalmar Allah.”
Ya kuma yaba wa dukkan mahalarta gasar, inda ya ce, “Hakikanin ruhin wannan gasa ba wai lambobin yabo kawai ba ne, amma neman ilimi da jarumtar shiga gasar.”
Gwamnan ya nuna godiya ga Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, da matarsa Hajiya Nana Kashim Shettima, da sauran manyan baƙi da suka bayar da gudunmawa wajen samun nasarar gasar.
Haka kuma, ya yaba da rawar da sarakunan gargajiya, shugabannin jami’o’i, malaman addinai da shugabannin siyasa suka taka wajen nasarar taron.
Manyan baƙi da suka halarci taron sun haɗa da matar Mataimakin Shugaban Ƙasa, Hajiya Nana Kashim Shettima, Gwamnan jihar Katsina, Alhaji Dikko Umar Radda, Mataimakin Gwamnan Jihar Sakkwato, Shehun Borno, Alhaji Abubakar Ibn Umar Garbai El-Kanemi, ‘yan Majalisun Tarayya da jihohi da malaman addini.

Babban abin da ya kayatar a bikin shi ne rabon kyaututtuka da lambobin yabo ga waɗanda suka yi nasara, wanda matar Mataimakin Shugaban Ƙasa ta gabatar.


