Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
  • Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya Afrika
  • NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika

Jihar Borno Ce Tayi Nasara A Gasan Karatun Al Qur’ani Na Kasa
Published: December 20, 2025 at 12:44 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jihar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya ce ta lashe matsayi na ɗaya a rukunin maza a Gasar Karatun Al-Qur’ani ta Ƙasa ta shekarar 2025, wadda aka gudanar a Maiduguri ƙarƙashin taken “Borno 2025.”

Wannan gasa ta zama abin tarihi, domin ita ce karo na 40 da ake gudanarwa a Najeriya kuma Borno ta yi nasarar karɓar baƙuncinta cikin nasara.

Yayin sanar da sakamakon gasar, Daraktan Cibiyar Nazarin addinin Musulunci ta Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato, Farfesa Abubakar Yelwa, ya bayyana Musa Ahmed Musa daga jihar Borno a matsayin zakaran a rukunin maza.

A rukunin mata kuma, Hafsat Muhammad Sada daga Jihar Kano ce ta zama Dawisu.

Gasar wadda ta ɗauki tsawon mako guda, ta samu mahalarta mutane 296 daga jihohi 30 na Najeriya, inda suka fafata a rukunai daban daban.

Da yake jawabi a bikin rufe gasar, Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana nasarar gudanar da gasar a matsayin alamar dawowar zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Borno.

Ya ce gasar ta nuna jajircewar al’ummar jihar wajen zaman lafiya, ilimi da koyarwar Musulunci.

“Nasarar ku ba kawai cin gasa ba ce,” in ji Gwamna Zulum ga waɗanda suka yi nasara, “amma wata babbar nasara ce da ta samo asali daga dogon lokaci na jajircewa, himma da girmama Kalmar Allah.”

Ya kuma yaba wa dukkan mahalarta gasar, inda ya ce, “Hakikanin ruhin wannan gasa ba wai lambobin yabo kawai ba ne, amma neman ilimi da jarumtar shiga gasar.”

Gwamnan ya nuna godiya ga Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, da matarsa Hajiya Nana Kashim Shettima, da sauran manyan baƙi da suka bayar da gudunmawa wajen samun nasarar gasar.

Haka kuma, ya yaba da rawar da sarakunan gargajiya, shugabannin jami’o’i, malaman addinai da shugabannin siyasa suka taka wajen nasarar taron.

Manyan baƙi da suka halarci taron sun haɗa da matar Mataimakin Shugaban Ƙasa, Hajiya Nana Kashim Shettima, Gwamnan jihar Katsina, Alhaji Dikko Umar Radda, Mataimakin Gwamnan Jihar Sakkwato, Shehun Borno, Alhaji Abubakar Ibn Umar Garbai El-Kanemi, ‘yan Majalisun Tarayya da jihohi da malaman addini.

Babban abin da ya kayatar a bikin shi ne rabon kyaututtuka da lambobin yabo ga waɗanda suka yi nasara, wanda matar Mataimakin Shugaban Ƙasa ta gabatar.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi
Next Post: Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Zuwa Jami’ar Sheikh Dahiru Bauchi

Karin Labarai Masu Alaka

Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu Najeriya
Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutun Sallar Azumi Afrika
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara Afrika
‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Cin Karensu Babu Babbaka A Najeriya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Bindiga A Mali Sun Kashe Direbobin Manyan Motoci Afrika
  • Wasan Dambe Ya Dau Sabon Salo A Jihar Inugu Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Murtala Garo Murnar Zama Mataimakin Gwamnan Kano Labarai
  • Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro Tsaro
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno Tsaro
  • Hukumar NAHCON Ta Kamallah Shirye Shiryen Hajjin 2026 A Kasar Saudiya Labarai
  • An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu Afrika
  • Amurka Zata Bada Gudumawar Kudi Dala Bilyan 10 Ga Ayyukan Kwamitin Wanzar Da Zaman Lafiyan Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.