Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta
Published: December 24, 2025 at 10:26 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Kungiyar Kawancen Kasashen Yankin Sahel yace tilas a biyo bayan kafa rundunar sojojin hadin guiwa ta kasashen da kaddamar da gagarumin farmaki a kan ‘yan ta’adda cikin ‘yan kwanakin da suke tafe a yankin da ta’addanci yayi tsanani.

Shugaban Burkina Faso, Kyaftin Ibrahim Traore, bayyi karin bayani akan wannan furuci nasa ba, a bayan da aka ayyana shi a zaman shugaban Kungiyar Kawancen Kasashen Yankin Sahel, kungiyar da kasashe 3 dake cikinta suka balle daga cikin kungiyar Tattalin Arzikin Afirka ta Yamma, ECOWAS, ko CDEAO, a wannan shekarar.

Kasashen Mali da Burkina Faso da Nijar sun fi fuskantar ta’addanci a yankin bakin iyakokinsu a yayin da wannan yanki na Sahel dake kudu da hamadar Sahara ya zamo inda aka fi ganin ayyukan ‘yan ta’adda masu alaka da al Qaida da kungiyar Daesh, watau ISIS.

Shugabannin kasashen uku sun cimma daidaituwa a taron kolinsu na ranar talata, a kan bunkasa hadin kan tsaro da na tattalin arziki, kuma a karshen makon nan, kasashen uku sun kaddanar da sabuwar bataliya ta hadin guiwa wadda zata yaki ‘yan ta’adda na yankin sannan ana sa ran zata kumshi dakaru dubu 5.

Shugaban Jamhuriyar Nijar, Abdourahamane Tchiani, yace kungiyarsu ta samu nasarar kawo karshen sojojin mamaya a cikin kasashensu, bisa dukkan alamu gugar zana yake yi kan shawarar da kasashen suka yanke na korar sojojin faransa da Amurka daga cikin kasashensu.

Tchiani ya kara da cewa babu wata kasa ko kungiya da a yanzu zata gaya musu abinda ya kamata su yi.

Yanzu dai kasashen uku, sun karkata ga kasare Rasha domin tallafa musu wajen ayyukan tsaron yankinsu.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya
Next Post: Amurka Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashe Hudu Domin Inganta Kiwon Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar Labarai
Shugaban Ƙasar Koriya Ta Arewa Ya Halarci Gwajin Makami Mai Linzamin Kasar Labarai
Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
Jaura Ta Bayyana A Wasu Jihohin Amurka Labarai
Shin Ko Ganawar Zelensky Da Macron Zata Haifar Da ‘Da Mai Ido? Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi Labarai
  • An Katse Intanet Da Wayar Tarho A Kasar Uganda Siyasa
  • Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
  • Majalisar Dattawan Amurka Ta Amince Da Wata Doka Amurka
  • Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
  • Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.