Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta
Published: December 24, 2025 at 10:26 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Kungiyar Kawancen Kasashen Yankin Sahel yace tilas a biyo bayan kafa rundunar sojojin hadin guiwa ta kasashen da kaddamar da gagarumin farmaki a kan ‘yan ta’adda cikin ‘yan kwanakin da suke tafe a yankin da ta’addanci yayi tsanani.

Shugaban Burkina Faso, Kyaftin Ibrahim Traore, bayyi karin bayani akan wannan furuci nasa ba, a bayan da aka ayyana shi a zaman shugaban Kungiyar Kawancen Kasashen Yankin Sahel, kungiyar da kasashe 3 dake cikinta suka balle daga cikin kungiyar Tattalin Arzikin Afirka ta Yamma, ECOWAS, ko CDEAO, a wannan shekarar.

Kasashen Mali da Burkina Faso da Nijar sun fi fuskantar ta’addanci a yankin bakin iyakokinsu a yayin da wannan yanki na Sahel dake kudu da hamadar Sahara ya zamo inda aka fi ganin ayyukan ‘yan ta’adda masu alaka da al Qaida da kungiyar Daesh, watau ISIS.

Shugabannin kasashen uku sun cimma daidaituwa a taron kolinsu na ranar talata, a kan bunkasa hadin kan tsaro da na tattalin arziki, kuma a karshen makon nan, kasashen uku sun kaddanar da sabuwar bataliya ta hadin guiwa wadda zata yaki ‘yan ta’adda na yankin sannan ana sa ran zata kumshi dakaru dubu 5.

Shugaban Jamhuriyar Nijar, Abdourahamane Tchiani, yace kungiyarsu ta samu nasarar kawo karshen sojojin mamaya a cikin kasashensu, bisa dukkan alamu gugar zana yake yi kan shawarar da kasashen suka yanke na korar sojojin faransa da Amurka daga cikin kasashensu.

Tchiani ya kara da cewa babu wata kasa ko kungiya da a yanzu zata gaya musu abinda ya kamata su yi.

Yanzu dai kasashen uku, sun karkata ga kasare Rasha domin tallafa musu wajen ayyukan tsaron yankinsu.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya
Next Post: Amurka Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashe Hudu Domin Inganta Kiwon Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Za’a Ninka Shekarun Zama A Gidan Kurkuku Ga Masu Auren Jinsi A Senegal Afrika
An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio Labarai
Tinubu Ya Jaddada Buƙatar Kare Rayukan ‘Yan Afirka A Taron ECOWAS Afrika
An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe  Afrika
Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026 Afrika
Shugaba Trump Yace Amurka Zata Janye Yaki Da Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Ta Kama Wasu ‘Yan Leken Asiri Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • An Gano Kwale-Kwalen Fir’auna A Birnin Masar Afrika
  • Isra’ila Zata Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran Afrika
  • Mutane 27 Sun Rasa Rayukan Su A Najeriya Afrika
  • Shirin Dare 26.11.2025 Rediyo
  • Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Wajen Hakar Ma’adanai Dake Jihar Filato Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.