Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe
Published: January 13, 2026 at 11:15 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta jihar Gombe ta fara duba lafiyar masu niyyar zuwa aikin Hajji na shekarar 2026 a Asibitin kwarerru na jihar Gombe.

An shirya wannan Duba lafiyar ne domin tantance halin lafiyar masu niyyar tafiya kasa mai tsarki ta Saudiyya, kafin a fara tafiya.

Da yake magana a wajen kaddamar da aikin duba lafiyar, Sakataren hukumar, Alhaji Sa’adu Hassan, ya bayyana cewa duba lafiyar wajibi ne, kuma yana daga cikin manyan sharuddan da ake buƙata kafin a fitar da bizar Hajji ga masu niyya.

Alhaji Sa’adu ya ƙara da cewa an kammala duk shirye-shiryen da suka dace tare da shugabancin Asibitin domin tabbatar da cewa aikin zai gudana lafiya ba tare da wata matsala ba.

Ya lura cewa duba lafiyar bana ya fi na shekarun baya zurfi, domin yana kunshe da gwaje-gwaje na mahimman sassan jiki, ciki har da na zuciya, domin tabbatar da cewa duk wanda zai tafi Hajji yana da ƙoshin lafiya.

Shi ma da yake jawabi, Daraktan Lafiya na Asibitin kwarerru na Gombe, Dr. Sambo Dawa, ya tabbatar da cewa dukkanin masu niyyar Hajji za su samu cikakken duba lafiya daga ƙwararrun ma’aikatan lafiya.

Dr. Dawa ya ce asibitin ya tanadi kayan aiki da ma’aikatan da suka dace domin gudanar da aikin yadda ya kamata bisa ka’idojin lafiya na ƙasa da ƙasa.

Wannan duba lafiyar zai taimaka wajen kare lafiyar alhazan jihar Gombe yayin aikin Hajjin 2026.

Kiwon Lafiya

Post navigation

Previous Post: Real Madrid: Ta Kori Xabi Alonso Bayan Rashin Nasara A Wasan Kofin Sfaniya
Next Post: Dalibai Sun Koma Makarantu A Wasu Jihohin Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
Gombe Da UNFPA Sun Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Don Yaƙi Da Cutar Fistula Da Tamowa Afrika
Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika
Ansamu Maganin Da Yake Rage Kitsen Jijiyoyi A Amurka Amurka
Afirka Ta Kudu Ta Samu Rigakafin Cutar Boro Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Na Yi Murabus Ne Don Amurka Ta Keta Haddin Iraniyawa Amurka
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
  • Sama da mutane dubu 500 ne yanbindiga suka kora daga gidajensu a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
  • Hukumar Zabe A Najeriya Ta Cigaba Da Rijistar Katin Zabe Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Zata Fara Gwajin Shan Kwaya Kafun Daukar Aiki Kiwon Lafiya
  • Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026, Labarai
  • Bana Ba Harka Ga ‘Yan-Wasan Kwallon Kafar Najeriya Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.