Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Ta Janye Sojojinta Daga Gabas Ta Tsakiya
Published: January 15, 2026 at 4:15 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Amurka ta fara janye wasu ma’aikata daga sansanonin sojanta a yankin gabas ta tsakiya, a bayan da wani babban jami’in Iran ya gargadi makwabtansu cewa Iran zata kai hari kan sansanonin Amurka idan har aka kai mata hari.

A yayin da hukumomi a birnin Teheran ke kokarin kwantar da wutar tarzoma mafi muni tun bayan juyin juya halin Islama da aka yi, Teheran tana son yin hannunka mai sanda ma shugaba Donald Trump da barazanarsa ta tsoma baki domin goyon bayan masu zanga zangar kin jinin gwamnati.

Wani jami’in Amurka da bai so a fadi sunansa ba yace Amurka tana kwashe ma’aikata daga wasu muhimman sansanoninta a saboda karuwar tankiya.

Wani jami’in soja a kasar yammaci yace a bisa dukkan alamu Amurka ta yanke shawarar zata kai ma kasar Iran farmaki, amma kuma yace irin wannan dabi’a gwamnatin Trump ta saba nunawa na haddasa yanayin kokwanto a kan zata kai ne ko ba zata kai harin ba.

Amma kuma a fadarsa ta White House, shugaba Trump ya nuna alamun kamar yana jira ya ga yadda lamarin zai wakana ne, trump yace wata majiya mai tushe ta fada masa cewa yawan kashe kashe ya ragu, kuma babu wani shirin da aka yi a yanzu na zartas da hukumcin kisa a kan mutane masu yawa.

Wasu jami’an Turai guda biyu ma sun ce watakila nan da sa’o’i 24 Amurka zata kai hari a kan kasar Iran haka ma wani jami’in gwamnatin bani Isra’ila yace da ala mun shugaba Trump ya yanke shawarar zai tsoma hannu a Iran, amma ba a san irin farmakin da zai kai ko kuma lokacin kaiwa ba.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Kasar Amurka Da Denmark Suna Rikici Akan Iyakar Greenland

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela Amurka
Kasar Rasha Ta Zargi Ukraine Da Kai Hari Gidan Shugaban Rasha Amurka
Wasu Lauyoyi Sunyi Murabus Yayin Gudanar Da Wata Shari’a A Kasar Amurka Amurka
An Yi Fashin Kaguwa Da Dodon-Kodi Na Miliyoyin Dalar Amurka Amurka
Sabon Ma’aikacin Tsaro Ne Ya Kashe Amurkawa Amurka
Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Amurka Ta Janye Sojojinta Daga Gabas Ta Tsakiya
  • Kasar Amurka Da Denmark Suna Rikici Akan Iyakar Greenland
  • Kasar Sham Ta Sallami Wasu Fararen Hula
  • Zaman Lafiya Yafara Dawowa A Sudan
  • Shugaban Kasar Uganda Yana Kokarin Mayar Da Mulkin Kasar Na Gado

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
  • Masu Ruwa da Tsaki akan Lamurran Siyasa sun Fara Maida Martani akan Matakin da Ministan Labaran Nigeria da wayar da kan Jama,a Idris Malagi na korar Daya Daga cikin Ma,aikatansa Saboda dalilai na Siyasa. da tsakiayar ranar Wannan larabace dai Mataimakin na Musamman akan yada Labarai ga Minista Malagi Malam Rani,u Ibrahim ya fitar da Wata sanarwar cewa Ministan ya Dakatar da Daya Daga cikin Ma,aikatansa Mai Suna Sa,idu Enagi Saboda ya fitar da Wani bayani a Kafar yada Labarai na sada zumunta dake Nuna Ministan ya shirya tsaf Domin takarar Gwamnan Jihar Neja a 2027. Malam Sa,idu Etsu Tsohon Dantakarar Shugaban cin Jam,iyyar APC a Nigeria Yace Matakin da Ministan ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu lokaci baiyi ba..ceu.. Shima Dattijon Siyasa a Jihar Neja Alh.Awaisu Giwa Kuta Yace Matakin da Ministan Labaran ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu Jihar Neja zaman Makoki Ake na fotinar Yan ta,adda ba wai Batun Neman Mukamin Siyasa ba..ceu .in.. To Sai jigon Jam,iyyar PDP Mai Adawa a Nigeria Hon.Yahaya Ability Yace Akwai kuskure Babba da Ministan ya tabka a dai dai Wannan Zamani na Siyasa duk da cewa Jihar Nejan na cikin Yanayi na masifar Yanbindiga..ceu..in .. Azaben Shekara ta 2023 Malagi ya kara yayi Takara Gwamnan Jihar Neja a jam,iyyar APC inda Gwamna Umar Bago ya kadashi a zaben fidda Gwani.
    Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa Najeriya
  • Jihohin Arewaci Sun Kafa Asusun Yaki Da Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sarkin Kagarko Ya Rasu Yana Da Shekaru 110 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
  • Gwamnan Neja Bago Na Cin Zarafin Talakawan Da Suka Zabe Shi Labarai
  • Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.