Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Mayakan RSF A Sudan Suna Sace Kananan Yara A Lokacin Yake-Yaken Kasar
Published: January 30, 2026 at 8:05 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 31, 2026

Wani bincike da kamfanin dillacin labarai na Reutres ya yi, ya bankado cewa Sojojin sa kai a Sudan sun sace yara lokacin da suka kwaci birnin al-Fashir a watan Octoba, da kuma lokacin da suka kai hare-hare a yankin na Darfur tun fara yakin basasar da ake ta gwabzawa tsakanin su da sojin kasar. An ce ma wani sa’in suna kashe iyayen yaran ne kafin su dauke su.

Wadanda abun ya faru a kan idon su sun shaidawa kamfanin dillacin Labarai na Reuters cewa, dakarun tawayen RSF sun fadawa iyayen yaran cewa za’a yi amfani da su ne a matsayin bayi don su yi kiwon dabbobi.

Rigima ta kaure ne tsakanin dakarun na RSF da sojojin Sudan tun watan Aprilun shekara ta 2023, kan wanda ya cancanta ya rike ragamar mulkin kasar msi arzikin albarkatu da yalwar kasar noma da kuma tasoshin jiragen ruwa a gabar da kogin bahar maliya.

Duk da cewa masu rajin kare hakki sun bada rahoton cewa duka bangarorin sun tafka laifukan yaki, ciki har da daukan yara don aiki a wajen daga, ba’a kawo rahoto kan sacewa da bautar da yara da kungiyar RSF da ‘yan kawancen ta ke yi ba.

Mutane 26 da abin ya faru a kan idon su, sun zanta da kamfanin dillacin labarai na Reuters ido da ido ko ta wayar tarho, bayan da suka tsere zuwa garin Tawila da ke arewacin Dafur ko kasar Chad. Sun yi bayanin abubuwan da suka faru, inda aka sace kalla yara 56 da shekarun su ya kama daga wata 2 zuwa shekara 17 tun a shekarar 2023.

Afrika, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kungiyar ISIS Ta Dauki Alhakin Harin Kasar Nijar
Next Post: Tattalin Arzikin Kasar Uganda Zai Bunkasa A Wannan Shekarar

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa A Djibouti Yau Juma’a Afrika
Shugaban Libya Ya Sayi Jirage Marasa Matuka Afrika
Donald Trump Yace Basu Cimma Matsaya Da Benjamin Natanyahu Ba Afrika
Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Dawo Da Kudaden Ma’aikata Afrika
Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamna Abba Kabir Ya Zabi Garo A Matsayin Mataimaki Afrika
  • Ana Sa Ran FIFA Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Najeriya Ta Shigar Kan DR Congo Wasanni
  • Majalisar Malaman Yarbawa Ta Yi Jimamin Rasuwar Babban Limamin Nuruddeen A Gombe Afrika
  • ‘Yan Sanda Sunce Mutum Daya Ne Yakai Hare-Haren Jami’ar Brown Da Kuma Na MIT Boston Amurka
  • Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai A Kasuwannin Duniya Yayi ƙasa Kadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamna Inuwa Yahaya Ya Rantsar Da Sabon Shugaban Ma’aikatan Jiha da Kwamishinoni 23 Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.