Wani bincike da kamfanin dillacin labarai na Reutres ya yi, ya bankado cewa Sojojin sa kai a Sudan sun sace yara lokacin da suka kwaci birnin al-Fashir a watan Octoba, da kuma lokacin da suka kai hare-hare a yankin na Darfur tun fara yakin basasar da ake ta gwabzawa tsakanin su da sojin kasar. An ce ma wani sa’in suna kashe iyayen yaran ne kafin su dauke su.
Wadanda abun ya faru a kan idon su sun shaidawa kamfanin dillacin Labarai na Reuters cewa, dakarun tawayen RSF sun fadawa iyayen yaran cewa za’a yi amfani da su ne a matsayin bayi don su yi kiwon dabbobi.
Rigima ta kaure ne tsakanin dakarun na RSF da sojojin Sudan tun watan Aprilun shekara ta 2023, kan wanda ya cancanta ya rike ragamar mulkin kasar msi arzikin albarkatu da yalwar kasar noma da kuma tasoshin jiragen ruwa a gabar da kogin bahar maliya.
Duk da cewa masu rajin kare hakki sun bada rahoton cewa duka bangarorin sun tafka laifukan yaki, ciki har da daukan yara don aiki a wajen daga, ba’a kawo rahoto kan sacewa da bautar da yara da kungiyar RSF da ‘yan kawancen ta ke yi ba.
Mutane 26 da abin ya faru a kan idon su, sun zanta da kamfanin dillacin labarai na Reuters ido da ido ko ta wayar tarho, bayan da suka tsere zuwa garin Tawila da ke arewacin Dafur ko kasar Chad. Sun yi bayanin abubuwan da suka faru, inda aka sace kalla yara 56 da shekarun su ya kama daga wata 2 zuwa shekara 17 tun a shekarar 2023.


