Abdu Mai Kaba Ya Ajiye Aikin Horas da Wikki Tourist fc Bauchi da ke Arewa maso gabas a Najeriya.
Bayan da ƙungiyar kwallon kafa ta Wikki Tourist fc Bauchi ta tashe canjaras da Katsina United 4-4 a wasan mako na 25 cikin gasar Firimiyar lig na Najeriya 25/26.
Ƙungiyar ta shiga rudani bisa irin maki da ta ke zubarwa a gida Wikki Tourist tayi canjaras a wasannin gida har guda 7 an shata a wasa daya a kakar wasan bana, jimillan makin da tayi a sara a gida 17, wadda hakan ya zamo babban kalu-bale a ƙungiyar kuma tana mataki na 15 da maki 29.
Inda wasu ki zargin maihoras da yanwasa Abdu Maikaba na rashin sanya Yan wasa a lokacin da ya dace, har ya kaima wasu magoya bayan Kulub din sukan fadi bakaken maganganu akan sa a zahiri da kuma shafin sada zumunta (Social media ) .na cin mutumcin sa
Saidai wasu masharhanta na gani cewa babu laifin Maikaba matsalar Wikki matsalace ta cikin gida, domin duk Shugaban da aka sauke yana da magoya baya da zasu tsangwami sabon shugaba suma a bangaren sabon babu shiri da wadda ya samesu a ciki musamman ƙungiyar Magoya baya saboda nan ta ke shima sabon shugaba zai sauke Jagororin magoya baya shima ya nada nasa wannan na daya daga cikin matsalolin Wikki ” inji masharhanta a jihar.
“Kuma anki ayi zaben Shuwagabannin magoya baya kamar yadda doka ya tanardar sai dai a bada rokon kwarya.
A gefe guda kuwa masu ruwa da tsaki akan harakar kwallon kafa a jihar wadda dasu aka kirkiri ƙungiyar sun daura laifine akan yadda aka sauka daga tsari da dokokin da aka kafa ƙungiyar.
Abdu Maikaba shi ya dawo da ƙungiyar kwallon kafa ta Wikki Tourist zuwa buga gasar Firimiyar lig na Najeriya
Abdu Maikaba Ya Ajiya Aikinsa a Wikki Tourist
Ga abunda ya rubuta

“Ina so in yi amfani da wannan dama domin sanar da hukumar gudanawar kungiyar Wikki Tourists F.C game da shawarar da na yanke na yin murabus daga matsayina na babban mai horaswa (Technical Adviser) na kungiyar, tun daga 09/02/2026 “inji Maikaba
Wannan shawara ta zama dole ne sakamakon dalilai kamar haka:
Rashin hadin kai:
Akwai rashin jituwa tsakanin masu ruwa da tsaki na kungiyar, wanda hakan ke sanya wahalar cimma manyan burin na kungiyar da ta sanya a gaba.
Saboda tsaron lafiya na ina fuskanci
barazanar a yayin gudanar da aikina daga wasu bangarorin magoya bayan kungiyar, bisa yadda suke mun a fili da kuma ta kafafen sada zumunta inji shi.
Saboda wadannan dalilai, na ga ya dace in dauki matakin ajiye aiki bayan na nemi shawarar iyalina.
Ina kuma amfani da wannan dama domin gode wa hukumar gudanawar kungiyar bisa damar da suka bani nayin aiki a wannan babban kulob. Ina fatan za a karbi murabus dina.


