Ranar Litinin, masu gabatar da kara a gaban babbar kotun kasa da kasa mai hukunta laifuffukan yaki, sun gayawa kotun cewa tsohon shugaban Phllipines Rodrigo Duterte, shine “jigo” a kisan dubban mutane lokacin mulkinsa, a lokacin da suke matsa kaimi na ganin an ci gaba da shari’ar sa.
Masu gabatar da kara a gaban kotun dake birnin Hague sun tuhumi Duterte da laifuffuka uku da suka hada da cin zarafin Bil’adama wadda suka ce kadan ne daga cikin mutanen da suka halaka karkashin ikonsa na yaki da masu shan kwaya da miyagun mutane ‘yan kasar.
Masu gabatar da karar suka ce, “Tilas ne a hukunta Mr. Duterte, domin wajibi ne kotu ta ci gaba da sauraron wannan shari’a.
Lauyan tsohon shugaban kasar Phillipines din Nicholas Kauffman, yace shari’ar bita da kullin siyasa ne, kuma ba’a ma fahimci Mr. Duterte bane.


