Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Kurdawa Sun Gargadi ‘Yan Uwansu Game Da Alaka Da Amurka Wajen Yakar Iran
Published: March 9, 2026 at 3:58 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A halin da ake ciki, Kurdawan kasar Sham ko Syria, sun gargadi ‘yan’uwansu na kasar Iran da kada su yarda su kulla kawance da Amurka wajen yakar Gwamnatin Iran.

Kurdawan na kasar Syria sun yi misali da irin halin da suka samu kansu a ciki, suna masu fadin cewa za a yi amfani da su ne kawai a kasar.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters yace rundunonin sa kai na Kurdawan Iran dake zaune a yankin arewacin Iraqi, sun gana a lokuta da dama da wakilan Amurka a cikin ‘yan kwanakin nan a kan kai farmaki kan dakarun kasar Iran a yankin yammacin kasar, yayin da Amurka da Isra’ila ke kai hare-hare ta sama.

Amma Kurdawan Syria, wadanda suka yi kawance da Amurka sun ja kunnen ‘yan’uwansu na Iran cewa za a jefa su a rana, a bar su, kamar yadda Amurka ta yi ma Kurdawan na Syria.

Wani Bakurde mai shekaru 45 mazaunin garein Qamishli na Kurdawa a arewa maso gabashin Syria, ya jaddada gargadi ga Kurdawan Iran cewa kada su yi kuskuren da Kurdawan Syria suka yi.

Afrika, Amurka, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini
Next Post: Rundunar Sojin Iran Tace Harin Amurka Ya Kashe Musu Sama Da Mutane Dari

Karin Labarai Masu Alaka

Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi Afrika
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Masu Zuba Jari A Birnin Paris Afrika
Shugabannin Darikar Anglican Sun Bada Sanarwar Kafa Sabuwar Majalisa Afrika
Sojin Israela Sunkai Hari Kan Falatsinawa Tsaro
Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
Sojojin Amurka Sunfara Isowa Gabas Ta Tsakiya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • Turkiyya Tana Gudanar Da Binciken Kasar Da Suka Kona Tutar Ta Tsaro
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Rasha Ta Gargadi Amurka Da Isra’ila Kan Harin Iran Afrika
  • Ana Sa Ran FIFA Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Najeriya Ta Shigar Kan DR Congo Wasanni
  • AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
  • Gwamnan Jihar Adamawa Fintiri Ya Koma APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.