Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Iran Zata Kai Hari Tashar Makamashin Ruwa A Gulf
Published: March 23, 2026 at 7:19 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A jiya Lahadi Iran ta bayyana cewa za ta kai hari kan tashar makamashi da na ruwa na ƙasashen maƙwabta a yankin Gulf, a matsayin martani idan Shugaban Amurka, Donald Trump, ya aiwatar da barazanar da ya yi na kai hari kan tashar wutar lantarki na Iran cikin sa’o’i 48, lamarin da ke ƙara tsananta rikicin da ya shafe makonni uku yana gudana.

Hasashen irin waɗannan hare-hare na ramuwar gayya kan kayayyakin more rayuwa na fararen hula na iya ƙara tsananta rikicin yankin, tare da girgiza kasuwannin duniya lokacin da za su sake buɗewa a safiyar Litinin.

An ji ƙararrawar gargadin hare-haren sama a sassan Isra’ila tun daga farkon safiyar Lahadi, domin sanar da zuwan makamai masu linzami daga Iran, bayan da mutane da dama suka jikkata a daren jiya sakamakon hare-hare biyu daban-daban a garuruwan Arad da Dimona da ke kudancin Isra’ila.

Sojojin Isra’ila sun ce bayan wasu sa’o’i sun fara kai hare-hare kan Tehran a matsayin martani.

Trump ya yi barazanar a daren jiya cewa zai “lalata gaba ɗaya” tashoshin samar da wutar lantarki na Iran idan Tehran ba ta buɗe mashigin ruwan Hormuz gaba ɗaya cikin sa’o’i 48 ba. Wannan na zuwa ne kusan kwana guda bayan ya yi magana kan “rage zafin yaƙin.” Ya kuma yi wannan sabuwar barazana ne a daidai lokacin da dakarun ruwan Amurka da manyan jirage masu sauka cikin ruwa ke kan hanyarsu zuwa yankin.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sarkin Gombe Ya Ziyarci Gwamna Inuwa Yahaya
Next Post: An Zargi Babban Mai Gabatar Da Kara A Kotun Duniya Ta ICC

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Ya Janye Karbar Kudin Fito Daga Wasu Kasashen Turai Amurka
Isra’ila Ta Kashe Babban Jami’in Tsaron Iran Ali Larjani Afrika
Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
Amurka Ta Bada Tabbacin Baiwa Ukraine Tsaron Na Shekaru 15 Amurka
Ankara Kai Wani Harin Bom Birnin Maiduguri Afrika
Jirgin Ruwa Ya Kife A Yammacin Kasar Gambiya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Gabatar Da Sabbin Kudurorin Kare Muhalli Da Gandun Daji A Gombe Afrika
  • Hukumar IMF Tana Naziri Domin Kara Bada Lamuni Ga Kasar Zambiya Afrika
  • An Kaddamar Da Rigakafin Cutar HIV AIDS A Kasar Zimbabwe Kimiya
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila Najeriya
  • Kasar Gambiya Ta Gayawa Kotun MDD Shirin Myanmar Akan Musulmai Afrika
  • Malaman Tsangaya A Gombe Sun Goyi Bayan Inuwa Yahaya Da Jamilu Gwamna Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.