Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Hamas Ta Kwance Damara
Published: March 28, 2026 at 8:50 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Karkashin shirin ganin Hamas ta kwance damara, za’a bukaci kungiyar mayakan ta kyale a rusa dukkan hanyoyin karkashin kasa data gina a Gaza, mataki da za’a gudanar daki daki cikin wata 8, kamar yadda yake kunshe cikin shirin da kwamitin wanzar da zaman lafiya da shugaban Amurka Donald ya kafa, ya gabatarwa kungiyar.

Kamar yadda kwamitin ya tsara, da farko kwararru daga yankin Falasdinu za su kama iko da matakan tsaro a Gaza, sannan daga bisani Isra’ila zata janye daga zirin, bayan da aka tabbatar da cewa, babu sauran makamai a zirin na Gaza.

Batun kwance damarar Hamas shine babban batu da yake hana ruwa gudu a shawarwari na aiwatar da shirin wanzar da zaman lafiya a Gaza da shugaba Trump ya gabatar, wadda idan aka yi haka zai jaddada yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma cikin watan oktban bara wanda ya tsaida yakin na tsawon shekaru biyu.

Hamas ta juma tana watsi da kiraye kirayen ta kwance damara, da mika makamanta da ta boye cikin hanyoyin karkashin kasa a Gaza. Isra’ila kuma tace ba zata janye daga Gaza ba har sai an tabbatar da cewa Hamas bata da sauran makamai

Wani jami’in Falasdinu wanda yake da kusanci da shawarwarin da ake yi yace shirin bashi da adalci, kuma yana ganin Hamas zata bukaci a yi wasu sauye sauye domin a kara inganta shi.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya
Next Post: Magungunan Cutar Kolera Sun Makale A Dubai

Karin Labarai Masu Alaka

Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato Labarai
Yunkurin Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi Na Kara Kankama A Najeriya Labarai
Tashoshin Mai Basa Iya Loda Mai A Rasha Labarai
Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
Sojin Saman Najeriya Sun Lalata Sansanonin ‘Yan Ta’adda Afrika
Gwamnatin Janhuriyar Nijar Ta Soke Lasisin Wasu Kamfanonin Dakon Mai Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC Najeriya
  • Gwamnatin Najeriya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci Afrika
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Taki Da Mai Ga Manoma Labarai
  • Mahaifiyar Nasiru El Rufai Ta Rasu Afrika
  • ‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke Wasanni
  • Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
  • Koriya Ta Arewa Ya Goyi Bayan Iran Wajen Zaben Sabon Jagora Mojtaba Khameni Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.