Karkashin shirin ganin Hamas ta kwance damara, za’a bukaci kungiyar mayakan ta kyale a rusa dukkan hanyoyin karkashin kasa data gina a Gaza, mataki da za’a gudanar daki daki cikin wata 8, kamar yadda yake kunshe cikin shirin da kwamitin wanzar da zaman lafiya da shugaban Amurka Donald ya kafa, ya gabatarwa kungiyar.
Kamar yadda kwamitin ya tsara, da farko kwararru daga yankin Falasdinu za su kama iko da matakan tsaro a Gaza, sannan daga bisani Isra’ila zata janye daga zirin, bayan da aka tabbatar da cewa, babu sauran makamai a zirin na Gaza.
Batun kwance damarar Hamas shine babban batu da yake hana ruwa gudu a shawarwari na aiwatar da shirin wanzar da zaman lafiya a Gaza da shugaba Trump ya gabatar, wadda idan aka yi haka zai jaddada yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma cikin watan oktban bara wanda ya tsaida yakin na tsawon shekaru biyu.
Hamas ta juma tana watsi da kiraye kirayen ta kwance damara, da mika makamanta da ta boye cikin hanyoyin karkashin kasa a Gaza. Isra’ila kuma tace ba zata janye daga Gaza ba har sai an tabbatar da cewa Hamas bata da sauran makamai
Wani jami’in Falasdinu wanda yake da kusanci da shawarwarin da ake yi yace shirin bashi da adalci, kuma yana ganin Hamas zata bukaci a yi wasu sauye sauye domin a kara inganta shi.


