Dakarun Amurka ta ruwa a ranar Litinin suka fara killace hanyoyin ruwa na kasar Iran, tare da hana jiragen ruwa shiga ko fita daga tashoshin ruwa na kasar, inji shugaba Donald Trump, Iran tayi barazanar zata rama kan kasashe makwabta a yankin Gulf, bayanda aka tashi baram baram a shawarwari da suka yi a Pakistan, da nufin kawo karshen yakin da suke gwabzawa.
Wani jami’in Amurka yace ana ci gaba da tuntubar juna da Iran, da nufin cimma yarjejeniya. Shi ma Prime Ministan Pakistan Shehbaz Sharif yace ana ci gaba da kokarin warware rikicin.
Saboda wannan yanayi da ake ciki, farashin mai ya sake cullawa sama da dala dari kan ko wace ganga, ba tare da an ga wata alamar za’a bude mashigin ruwa na Hormuz nan take ba, domin sassauta kassara jigilar mai mafi girma a tarihi, da kuma ci gaba da nuna damuwa kan dorewar yarjejeniyar tsagaita wuta na mako biyu da aka cimma cikin makon jiya.
Trump ya fada a jiya Litnin cewa Iran ta yi tuntuba a jiyan tana son a kulla yarjejeniya, amma ba zai amince da duk wata yarjejeniyar da zata kyale Iran ta mallaki makaman Nukiliya ba.
Tun bayan da Amurka da Isra’ila suka kaddamar da hare hare akan Iran ranar 28 ga watan Febwairu, Iran ta rufe mashigin ruwa na Hormuz ga dukkan jiragen ruwa in banda nata, tana mai cewa ba jirgin ruwan da za’a kyale ya wuce ba tare da izininta ba tare da an biyan wani hasafi.
Trump yace Washington zata hana duk wani jirgin ruwa daga Iran, da duka jiragen da suka biya Farisa wani kudi wuce wa, kuma duk wani karamin jirgin ruwan Iran masu kai hari da ya yi kusa da jiragen ruwa yaki na Amurka zai zama tarihi.


