Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Dakarun Tsaron Ruwan Amurka Sunfara Killace Hanyoyi
Published: April 14, 2026 at 8:19 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Dakarun Amurka ta ruwa a ranar Litinin suka fara killace hanyoyin ruwa na kasar Iran, tare da hana jiragen ruwa shiga ko fita daga tashoshin ruwa na kasar, inji shugaba Donald Trump, Iran tayi barazanar zata rama kan kasashe makwabta a yankin Gulf, bayanda aka tashi baram baram a shawarwari da suka yi a Pakistan, da nufin kawo karshen yakin da suke gwabzawa.

Wani jami’in Amurka yace ana ci gaba da tuntubar juna da Iran, da nufin cimma yarjejeniya. Shi ma Prime Ministan Pakistan Shehbaz Sharif yace ana ci gaba da kokarin warware rikicin.

Saboda wannan yanayi da ake ciki, farashin mai ya sake cullawa sama da dala dari kan ko wace ganga, ba tare da an ga wata alamar za’a bude mashigin ruwa na Hormuz nan take ba, domin sassauta kassara jigilar mai mafi girma a tarihi, da kuma ci gaba da nuna damuwa kan dorewar yarjejeniyar tsagaita wuta na mako biyu da aka cimma cikin makon jiya.

Trump ya fada a jiya Litnin cewa Iran ta yi tuntuba a jiyan tana son a kulla yarjejeniya, amma ba zai amince da duk wata yarjejeniyar da zata kyale Iran ta mallaki makaman Nukiliya ba.

Tun bayan da Amurka da Isra’ila suka kaddamar da hare hare akan Iran ranar 28 ga watan Febwairu, Iran ta rufe mashigin ruwa na Hormuz ga dukkan jiragen ruwa in banda nata, tana mai cewa ba jirgin ruwan da za’a kyale ya wuce ba tare da izininta ba tare da an biyan wani hasafi.

Trump yace Washington zata hana duk wani jirgin ruwa daga Iran, da duka jiragen da suka biya Farisa wani kudi wuce wa, kuma duk wani karamin jirgin ruwan Iran masu kai hari da ya yi kusa da jiragen ruwa yaki na Amurka zai zama tarihi.

Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tsohon Jagoran Masu Kishin Kasa A Hungry Ya Amince Da Shan Kaye
Next Post: Kawayen Amurka Bazasu Shiga Matakin Shugaba Trump Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Dakarun Sakai A Kasar Sudan Sun Kashe Mutane 28 A Wani Farmaki Afrika
Trump Zai Sasanta Tsakanin Masar Da Habasha Amurka
Makiyaya Sun Shiga Matsala Sakamakon Fari A Kasar Kenya Afrika
Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
Kasar Afirka Ta Kudu Ta Gayyaci Sabon Jakadan Amurka Afrika
Akwai Yiwuwar Iran Da Amurka Su Cimma Matsayar Dakatar Da Shirin Nukiliya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotun Tarayya Tabada Belin Nasiru El Rufai
  • Dan Hamayya Ya Amince Da Faduwa A Zaben Kasar Benin
  • Zabebben Shugaban Hungary Yace Zaidawo Da Tsarin Dimokraɗiyya
  • Papa Roma Leo Yace Zai Cigaba Da Sukan Yake Yake
  • Kawayen Amurka Bazasu Shiga Matakin Shugaba Trump Ba

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hotunan Hawan Sallah A Masarautar Bauchi Afrika
  • Majami’ar Anglican Zasuyi Taron Zaben Sabon Shugaba Afrika
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Karu A Karshen 2024 Rediyo
  • Wani Alkali A Kotun Amurka Ya Dakatar Da Kudurin Shugaba Trump Afrika
  • Ministan Harkokin Wajen Rasha Dana Iran Sun Tattauna Don Kawo Karshen Yaki A Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati Labarai
  • Farashin Danyen Mai Ya Farfado Fiye Da Kashi Daya Sauran Duniya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.