Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sauya Sunan Lafarge Africa Zuwa HBM Nigeria Plc Zai Samar Da Cigaba – Sarkin Fulanin Gombe Afrika
  • An Karrama Darakta Janar Na DSS Bisa Ƙoƙarinsa Na Inganta Alaƙar Hukumomin Tsaro Da Kafafen Yaɗa Labarai Afrika
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Zata Raba Taki Ga Manoma Afrika
  • Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe Afrika
  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya Afrika

Bayan Shekaru Biyar, Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Gano Motar da Aka Sace A Fatakwal
Published: June 20, 2026 at 9:49 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, ya bayyana cewa jami’an Sashen Binciken Sirri (SID) na rundunar, tare da haɗin gwiwar jami’an Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC), sun gano motar ne yayin wani aikin tantance bayanan motoci a Ofishin Ba da Lasisin Motoci na Hukumar Haraji ta Jihar Gombe a ranar 8 ga Yunin 2026.

Sanarwar ta ce yayin binciken bayanan motar mai lambar rajista FH823PHC, an gano alamun da suka nuna cewa motar na da alaƙa da rahoton sata.

Binciken farko ya tabbatar da cewa motar mallakin Misis Cecilia A. Duru ce, mazauniyar Akwaka Lane da ke Rumuodumaya a Fatakwal, kuma an sace ta ne a ranar 17 ga Satumban 2021.

Binciken da rundunar ta gudanar ya nuna cewa an kai motar zuwa Jamhuriyar Nijar a shekarar 2023. Daga bisani kuma an dawo da ita Najeriya ta Karamar Hukumar Illela da ke Jihar Sokoto a ranar 17 ga Oktoban 2025.

Bayan haka, an sayar da motar a Jihar Kaduna kafin daga ƙarshe a kawo ta Gombe domin sake yi mata rajista.

Rundunar ta ce bincike na ci gaba da nufin gano tare da cafke duk waɗanda ake zargi da hannu a satar motar da kuma safararta ba bisa ƙa’ida ba.

Haka kuma, rundunar ta tabbatar wa al’umma da cewa za ta ci gaba da ɗaukar matakan kare rayuka da dukiyoyi, tare da jan hankalin masu sayen motoci da su tabbatar da sahihancin takardun mallaka da bayanan mota daga hukumomin da suka dace kafin su kammala ciniki.

Sanarwar ta ƙara da cewa za a sanar da jama’a duk wani sabon ci gaba da aka samu yayin da bincike ke gudana.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe
Next Post: Gwamnatin Tarayyar Najeriya Zata Raba Taki Ga Manoma

Karin Labarai Masu Alaka

EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai
Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika
Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya Afrika
Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sauya Sunan Lafarge Africa Zuwa HBM Nigeria Plc Zai Samar Da Cigaba – Sarkin Fulanin Gombe
  • An Karrama Darakta Janar Na DSS Bisa Ƙoƙarinsa Na Inganta Alaƙar Hukumomin Tsaro Da Kafafen Yaɗa Labarai
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Zata Raba Taki Ga Manoma
  • Bayan Shekaru Biyar, Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Gano Motar da Aka Sace A Fatakwal
  • Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Za’ayi Auren Zawarawa Dubu Uku A Kano Afrika
  • Fadar Sarkin Musulmi: Talata Ne 1 Ga Watan Sha’aban Na 1447AH Najeriya
  • NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
  • Akwai Alamar Shawarwari Tsakanin Amurka Da Turai Zai Kawo Karshen Yakin Rasha Amurka
  • Gwamna Abba Ya Gana Da Kwankwaso Kamun Ganawarsa Da Tinubu Siyasa
  • An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya Afrika
  • Samar Da Albarkatun Mai Ya Ragu A Iraq Afrika
  • ‘Yan Uwan Wadanda Aka Kashe Sunkai Kara Kotu Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.