A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, ya bayyana cewa jami’an Sashen Binciken Sirri (SID) na rundunar, tare da haɗin gwiwar jami’an Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC), sun gano motar ne yayin wani aikin tantance bayanan motoci a Ofishin Ba da Lasisin Motoci na Hukumar Haraji ta Jihar Gombe a ranar 8 ga Yunin 2026.

Sanarwar ta ce yayin binciken bayanan motar mai lambar rajista FH823PHC, an gano alamun da suka nuna cewa motar na da alaƙa da rahoton sata.
Binciken farko ya tabbatar da cewa motar mallakin Misis Cecilia A. Duru ce, mazauniyar Akwaka Lane da ke Rumuodumaya a Fatakwal, kuma an sace ta ne a ranar 17 ga Satumban 2021.
Binciken da rundunar ta gudanar ya nuna cewa an kai motar zuwa Jamhuriyar Nijar a shekarar 2023. Daga bisani kuma an dawo da ita Najeriya ta Karamar Hukumar Illela da ke Jihar Sokoto a ranar 17 ga Oktoban 2025.
Bayan haka, an sayar da motar a Jihar Kaduna kafin daga ƙarshe a kawo ta Gombe domin sake yi mata rajista.
Rundunar ta ce bincike na ci gaba da nufin gano tare da cafke duk waɗanda ake zargi da hannu a satar motar da kuma safararta ba bisa ƙa’ida ba.

Haka kuma, rundunar ta tabbatar wa al’umma da cewa za ta ci gaba da ɗaukar matakan kare rayuka da dukiyoyi, tare da jan hankalin masu sayen motoci da su tabbatar da sahihancin takardun mallaka da bayanan mota daga hukumomin da suka dace kafin su kammala ciniki.
Sanarwar ta ƙara da cewa za a sanar da jama’a duk wani sabon ci gaba da aka samu yayin da bincike ke gudana.


