Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

CP Chuso Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Gwiwar Hukumomin Tsaro A Gombe
Published: August 14, 2026 at 7:49 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya karɓi Kwamishinan Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida da Harkokin Gida na jihar, Alhaji Adamu Dishi Kupto, a wata ziyarar sanayya da ya kai hedikwatar rundunar ‘yan sandan jihar.

Ziyarar ta kasance wata dama ta ƙarfafa haɗin gwiwa da zurfafa hulɗa tsakanin hukumomin tsaro da ma’aikatar, domin ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, tsaro da kare lafiyar al’umma a faɗin Jihar Gombe.

Da yake jawabi yayin ziyarar, CP Umar Ahmed Chuso ya nuna godiyarsa ga Kwamishinan bisa ziyarar, tare da jaddada aniyar rundunar ‘yan sandan na ci gaba da aiki kafada-da-kafada da ma’aikatar da sauran masu ruwa da tsaki wajen yaƙi da laifuka da magance matsalolin tsaro.

Ya kuma jaddada muhimmancin musayar bayanan sirri, gaggauta mayar da martani ga barazanar tsaro, haɗa kai da al’umma da kuma gudanar da ayyukan tsaro cikin tsari guda domin tunkarar sabbin ƙalubalen tsaro.

A nasa jawabin, Kwamishinan Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida da Harkokin Gida, Alhaji Adamu Dishi Kufto, ya yaba da ƙoƙarin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a jihar.

Ya yi alkawarin ci gaba da ba rundunar ‘yan sandan da sauran hukumomin tsaro cikakken goyon baya da haɗin kai, domin cimma burin samar da jihar Gombe mai aminci da kwanciyar hankali.

Ziyarar ta ƙare da sake jaddada ƙudurin ɓangarorin biyu na ƙarfafa haɗin gwiwa da kuma samar da hanyoyin tunkarar sabbin ƙalubalen tsaro a Jihar Gombe.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
Next Post: Pads To Prosperity: NEDC Ta Horar Da Mata 280 Kan Kera Pads A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Taron Masu Mu’amala Da Kafar Facebook A Kano Afrika
Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika
Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro Tsaro
An Farmaki ‘Yan Bindiga Da Dama A Jihar Zamfara Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika
  • Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu Afrika
  • Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20 Afrika
  • An Kashe Mayakan Sakai 67 A Pakistan Sauran Duniya
  • An Bude Kamfanin Sarrafa Ma’adanai A Kasar Mozambique Labarai
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Yi Ma Wasu Mutane Yankan Rago A Jihar Neja Labarai
  • Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist
    Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Ta Tura Mutane 386 Gidan Yari Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.