Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sanda, Sojoji Da DSS Sun Ceto ‘Yan NYSC Da Aka Sace A Kogi Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Al’umma Su Kiyaye Doka Yayin Bikin Takutaha Afrika
  • RUWASSA Ta Hada Masu Ruwa Da Tsaki Domin Inganta Aiwatar Da Shirin NG-SURWASH Afrika
  • Rundunar ’Yan Sandan Bauchi Ta Kama Dattijo Kan Zargin Cin Zarafin Yarinya ’Yar Shekara 8 Afrika
  • Gwamna Inuwa Yahaya Ya Jaddada Haƙuri Da Fahimtar Juna A Siyasa Afrika

Damara Ya Tallafa Wa Gasar Karatun Al-Qur’ani Da Naira Miliyan Biyar A Bambam
Published: August 30, 2026 at 9:15 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Dan siyasar nan, Jerry Joseph Damara, ya bayar da tallafin naira miliyan biyar domin tallafa wa taron karatun Al-Qur’ani na shekara-shekara da ƙungiyar Izala ke gudanarwa a garin Bambam, ƙaramar hukumar Balanga ta jihar Gombe dake arewa maso Gabashin Najeriya

Damara ya bayar da tallafin ne yayin da ya halarci taron addinin, inda ya bayyana karatun Al-Qur’ani a matsayin muhimmin aiki na ibada da ke ƙarfafa kyawawan ɗabi’u, zaman lafiya da haɗin kan al’umma.

Ya ce tallafin nasa ya nuna yadda yake ƙoƙarin inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban, tare da kula da jin daɗin al’ummar da yake wakilta ba tare da la’akari da bambancin addini ba.

Damara ya kuma tabbatar wa al’ummar Balanga cewa zai ci gaba da jajircewa wajen samar da ci gaba mai ɗauke da kowa, yana mai cewa wakilcinsa zai mayar da hankali ne kan ayyuka da shirye-shiryen da za su inganta rayuwar al’umma.

Shugabannin al’umma da malaman addinin Musulunci da suka halarci taron sun yaba da tallafin, inda suka bayyana shi a matsayin abin da ya zo a lokacin da ya dace kuma mai karimci.

Sun yi kira ga sauran masu ruwa da tsaki da masu rike da mukaman gwamnati da su yi koyi da irin wannan hali na tallafa wa ayyukan da ke inganta rayuwar ruhaniya da zamantakewar al’umma.

An kuma gudanar da addu’o’i domin samun zaman lafiya, ci gaba da wadata a Najeriya, tare da roƙon Allah Ya ci gaba da ba Damara nasara a ayyukan da yake yi wa al’umma.

Daga cikin manyan baki da suka halarci taron akwai Sakataren Gwamnatin Jihar Gombe, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi; ‘yar takarar jam’iyyar APC a mazabar tarayya ta Kaltungo/Shongom, Hajiya Fatima Binta Bello; tsohon mataimakin gwamnan jihar, Thaanda Jason Rubainu; da mai bai wa Gwamna shawara kan harkokin ƙarfafa matasa, Iliya Suleiman, da sauran baki.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sana'o'i, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamna Inuwa Yahaya Ya Jaddada Haƙuri Da Fahimtar Juna A Siyasa
Next Post: Rundunar ’Yan Sandan Bauchi Ta Kama Dattijo Kan Zargin Cin Zarafin Yarinya ’Yar Shekara 8

Karin Labarai Masu Alaka

Wani Jami’in Iran Yace Amurka Taso Kanta A Tattaunawar Tsagaita Wuta Amurka
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro Labarai
Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika
Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Majalisar Dottawa Ta Kafa Komitin Dokar Zabe Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sanda, Sojoji Da DSS Sun Ceto ‘Yan NYSC Da Aka Sace A Kogi
  • Rundunar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Al’umma Su Kiyaye Doka Yayin Bikin Takutaha
  • RUWASSA Ta Hada Masu Ruwa Da Tsaki Domin Inganta Aiwatar Da Shirin NG-SURWASH
  • Rundunar ’Yan Sandan Bauchi Ta Kama Dattijo Kan Zargin Cin Zarafin Yarinya ’Yar Shekara 8
  • Damara Ya Tallafa Wa Gasar Karatun Al-Qur’ani Da Naira Miliyan Biyar A Bambam

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
  • Ambaliyar Ruwa Ya Tilastawa Dubban Jama’a Rasa Muhallensu A Morocco Afrika
  • Matar El-Rufai Ta Roƙi Tinubu Ya Tabbatar An Yi Wa Mijinta Adalci Afrika
  • Farashin Danyen Mai Ya Farfado Fiye Da Kashi Daya Sauran Duniya
  • NFF, Ta Umarci Tawagar Masu Horas Da Super Falcons Su Sauka Daga Bakin Aiki Nan Take Wasanni
  • Ministocin Kasar Asia Zasu Gudanar Da Taro A Kasar Malaysia Tsaro
  • Nasarawa United Ta Kai Wasan Kusa da Ƙarshe Na Gasar Gusau/Ahlan 2026 Wasanni
  • Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.