Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Afirka Ta Kudu Ta Samu Rigakafin Cutar Boro
Published: February 6, 2026 at 8:35 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kasar Afirka ta kudu ta sanar da samun allurar rigakafi na farko cikin shekaru 20 kan cutar boro, (foot and mouth disease) a turance, yayin da take neman bunkasa sarrafa maganin rigakafin a cikin gida, don tunkarar barkewar annobar mafi muni a shekaru masu yawa.

Cutar boro, cuta ce da ake saurin dauka, Wadda kuma Shanu zasu iya kamuwa da ita.

Tana sa kuraje a baki da kofato masu radadi da ciwo. Duk da cewa bata fiye jawo mutuwar shanun ba, amma tana dakile amfanin da ake samu daga dabbobin, kama da haihuwa ko samun madara.

Rigakafin, wadda hukumar binciken aikin noma ta Afirka ta Kudu ta samar, wani bangare ne na kudurin da kasar ke da shi na yiwa kashi 80 cikin 100 na shanun ta da suka kai kimanin miliyan 12 allura.

Hukumar zata rika samar da allurai 20,000 kowanne mako, daga watan Maris na wannan shekarar, har ta kara wa’adin zuwa 200,000 a shekarar 2027.

Afrika, Kiwon Lafiya

Post navigation

Previous Post: Makiyaya Sun Shiga Matsala Sakamakon Fari A Kasar Kenya
Next Post: Akwai Nasara A Tattaunawar Da Akeyi Tsakanin Iran Da Amurka

Karin Labarai Masu Alaka

Ruwan Sama Yayi Ajalin Daruruwan Mutane A Afirka Ta Kudu Afrika
Hari Akan Wata Mashaya Ya Rutsa Da Mutane 9 A Afirka Ta Kudu Afrika
Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20 Afrika
Kasar Togo Ta Kori Paul Henri Damiba Zuwa Kasar Sa Ta Haihuwa Afrika
Manoma Suna Fuskantar Barazanar Karyewa A Kasar Ghana Afrika
Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet
  • Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Abba Kabir Yusuf Ya Koma Jam’iyar APC Siyasa
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni
  • Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila Najeriya
  • ‘Yan Kasar Cuba Sunyi Zanga Zanga A Ofishin Jakadancin Amurka Amurka
  • Gwamnatin Jihar Yobe: Ana Cin Zarafin Fursunoni A Gidan Gyaran Halin Potiskum Tsaro
  • Anyi Jefe-Jefe Yayin Rangadin Messi, A Indiya Wasanni
  • Ba Mamaki APC Ta Kafa Tarihi A Ranar Litinin Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.