Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia
Published: December 25, 2025 at 7:33 AM | By: Bala Hassan

Amurka ta sanya hanu kan sabbin yarjejeniyoyin kan kiwon lafiya da kasashen Madagascar, Saliyo, da Botswana, da kuma Ethiopia, wadda adadin kudaden da shirin zai bukata suka kai kusan dala bilyyan 2 da milyan 300, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fada a ranar talata.

A cikin watan Nuwambana bana ne gwamnatin shugaba Trump ta bayyana wani sabon tsarin tallafi gameda tallafin Amurka take bada wa ga kasashen ketare, da ya fi maida hankali wajen ganin kasashen da take taimakawa suna daukan hakkin kula da kiwon lafiyar kasashen su.

A cikin ko wace yarjejeniya ta kunshi sharudda da suka hada da aiwatar da ita sau da kafa, da kuma matakan ladabtarwa idan aka kaucewa yarjejeniyar, auna ci gaba da ake samu wajen ganin bayan barazana daga wasu cututtuka, da kuma kaucewa dogaro kan tallafin  da Amurka take bayarwa, kamar yadda ma’aiktar harkokin wajen Amurka ta fada a cikin wata sanarwa data fitar.

A duka yarjejeniyoyin Amurka ta kuduri anniyar zata kashe kudi dala bilyan daya da milyan dari hudu, yayinda kasashen hudu su  kuma za su kashe dala milyan dari tara daga aljehunansu.

Ofishin jakdancin Amurka dake Abidjan babban birnin kasar Ivory Coast ta ce sanya hanu kan yarjejeniyar kiwon lafiya na tsawon shekaru biyar da kasar, za’a gudanar da shi ranar Alhamis idan Allah ya kai mu.

Kamar yadda ofishin jakadancin ya ci gaba da cewa, yarjejeniyar an tsara ta ne da nufin karfafa hanyoyin gano bullar cututtuka da samar da ma’aikata, ta kara da cewa, Amurka zata samarda kudi dala milyan 273, Ivory coast kuma zata bada kudi bilyan 252 na kudin sefa.

Ahalinda ake ciki kuma, matakin janye jakadu masu yawa daga kasashen Afirka da suke kudu da hamadar sahara da Amurka tayi, zai bar Washington bata da manyan kwararru a kusan rabin kasashe da suke yankin, matakin da zai kara dagula yunkurin aiwatar da burin gwamnatin TRump a yankin da yake fama da juyin mulkin soja.

Tun fara aikin gwamnatin Trump, hukumomi a Washington suka bada karfi wajen gudanr da harkokin kasuwanci maimakon bada karfi kan tallafi.

Shugaba Trump ya maida karfi wajen ganin an cimma zaman lafiya, da kuma sanya hanu kan yarjejeniyin samarda muhmman albarkatun kasa, maimakon tallafi.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Netanyahu: Zamu Kashe Dala Billiyan $110 Cikin Shekaru Hudu Don Kera Makamai
Next Post: Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC

Karin Labarai Masu Alaka

Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali Afrika
An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kungiyar Cigaban Al’ummar Tangale Tace Bata Goyon Bayan Kai Ziyara Wa Gwamnan Gombe Labarai
  • Tattalin Arzikin Kasar Congo Ya Bunkasa Labarai
  • Shugaban Ƙasar Djibouti Ya Sake Lashe Zaben Shugaban Kasar Afrika
  • Gwamnatin Trump Ta Karawa Iran Wasu Takunkumai Amurka
  • Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto Labarai
  • An Kama Masu Fasa Kaurin Gawayi A Malawi Afrika
  • Zaizayar Kasa Tayi Ajalin Mutane 200 A Kasar Congo Afrika
  • Ko Arsenal Zata Iya Lashe Gasar Firimiya lig Na Bana Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.