Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali
Published: January 24, 2026 at 9:24 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Babban Hafsan Sojin Ƙasarln Najeriya, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya yi gargaɗi mai tsanani ga masu aikata laifuka da ke tayar da hankalin al’umma a faɗin ƙasar, inda ya ce za su fuskanci ƙarfin sojoji matuƙar ba su tuba daga munanan ayyukansu ba.

Fiye da sojojin musamman dubu ɗaya (1,000) ne aka ƙara tura wa fagen yaƙi domin ƙarfafa ayyukan tsaron cikin gida da ake gudanarwa a sassa daban-daban na ƙasar.

Babban Hafsan Sojin ya bayyana hakan ne yayin bikin kammala atisayen Exercise Restore Hope 9 da aka gudanar a sansanin rundunar sojin Najeriya da ke Kachia.

Ya jaddada cewa rundunar sojin ƙasa za ta ci gaba da tinkarar duk wani ɓangare na masu tada fitina, inda ya ce duk masu aikata laifi za su gamu da ƙarfin da za su iya jurewa, har sai sun daina munanan ayyukansu kuma sun tuba.

Ya kuma tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa rundunar sojin ƙasa za ta ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamna Ododo Ya Gargadi Sarakunan Gargajiya
Next Post: Najeriya Da Amurka Sun Amince Su Haɗa Kai Don Inganta ’Yancin Addini Da ƙarfafa Tsaro A Nijeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai
Jihar Kano Tayi Rashin ‘Yan Majalisu Biyu Najeriya
Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai Najeriya
Kamfanin NNPC Yana Tattaunawa Da Wani Kamfanin Kasar China Labarai
Sojin Najeriya Da ‘Yan Ta’adda Sunyi Taho Mugama Najeriya
Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
  • CAF Ta Hukunta Samuel Eto’o AFCON 2025 Labarai
  • Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
  • Shin Ko Ganawar Zelensky Da Macron Zata Haifar Da ‘Da Mai Ido? Labarai
  • Kamfanin NNPC Yana Tattaunawa Da Wani Kamfanin Kasar China Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu Labarai
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Gyara Dokar Kasafin Kudi Labarai
  • Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.