Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta
Published: December 24, 2025 at 10:26 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Kungiyar Kawancen Kasashen Yankin Sahel yace tilas a biyo bayan kafa rundunar sojojin hadin guiwa ta kasashen da kaddamar da gagarumin farmaki a kan ‘yan ta’adda cikin ‘yan kwanakin da suke tafe a yankin da ta’addanci yayi tsanani.

Shugaban Burkina Faso, Kyaftin Ibrahim Traore, bayyi karin bayani akan wannan furuci nasa ba, a bayan da aka ayyana shi a zaman shugaban Kungiyar Kawancen Kasashen Yankin Sahel, kungiyar da kasashe 3 dake cikinta suka balle daga cikin kungiyar Tattalin Arzikin Afirka ta Yamma, ECOWAS, ko CDEAO, a wannan shekarar.

Kasashen Mali da Burkina Faso da Nijar sun fi fuskantar ta’addanci a yankin bakin iyakokinsu a yayin da wannan yanki na Sahel dake kudu da hamadar Sahara ya zamo inda aka fi ganin ayyukan ‘yan ta’adda masu alaka da al Qaida da kungiyar Daesh, watau ISIS.

Shugabannin kasashen uku sun cimma daidaituwa a taron kolinsu na ranar talata, a kan bunkasa hadin kan tsaro da na tattalin arziki, kuma a karshen makon nan, kasashen uku sun kaddanar da sabuwar bataliya ta hadin guiwa wadda zata yaki ‘yan ta’adda na yankin sannan ana sa ran zata kumshi dakaru dubu 5.

Shugaban Jamhuriyar Nijar, Abdourahamane Tchiani, yace kungiyarsu ta samu nasarar kawo karshen sojojin mamaya a cikin kasashensu, bisa dukkan alamu gugar zana yake yi kan shawarar da kasashen suka yanke na korar sojojin faransa da Amurka daga cikin kasashensu.

Tchiani ya kara da cewa babu wata kasa ko kungiya da a yanzu zata gaya musu abinda ya kamata su yi.

Yanzu dai kasashen uku, sun karkata ga kasare Rasha domin tallafa musu wajen ayyukan tsaron yankinsu.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya
Next Post: Amurka Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashe Hudu Domin Inganta Kiwon Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Anyi Taho Mugama Tsakanin ‘Yan Sandan Turkiyya Da ‘Yan Kungiyar ISIS Afrika
Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum Afrika
Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
Menene Illar Yada Labaran Karya A Kafofin Sada Zumunta Na Zamani Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Talauci Ya Ragu A Tsakanin Al’ummar Jihar Jigawa Siyasa
  • Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar Afrika
  • Anyi Rashin ‘Yan Jarida 6 A Jihar Gombe Sakamakon Hatsarin Mota Labarai
  • Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen Afrika
  • An Sako Dan Siyasar Kasar Venezuela Daga Gidan Yari Labarai
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai
  • Salmanu: Ci Gaban Wikki Tourist FC Shine A Gaba Na Wasanni
  • Yau Lahadi Ake Gudanar Da Zabe A Kasar Myanmar Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.