Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

CAF Ta Hukunta Samuel Eto’o AFCON 2025
Published: January 16, 2026 at 8:26 AM | By: Bala Hassan

An dakatar da tsohon tauraron kwallon kafa na Kamaru Samuel Eto’o na wasanni hudu tare da cin tararsa dala $20,000 (£14,960) bayan kwamitin ladabtarwa na Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (Caf) ya same shi da laifin rashin da’a.

Sanarwar Caf ta ce Eto’o, wanda yanzu shine shugaban hukumar kwallon kafa ta kasarsa Kamaru (Fecafoot), ya karya ka’idojinta na wasanni a lokacin wasan kusa da na karshe na gasar cin kofin kasashen Afirka ta 2025 tsakanin Kamaru da Morocco.

An ruwaito cewa tsohon dan wasan gaban Barcelona da Inter Milan ya nuna fushinsa kan wasu daga cikin shawarwarin da jami’an suka yanke yayin da Indomitable Lions ta sha kashi 2-0 a hannun masu masaukin baki Ƙasar Moroko.

Shugaban Caf Patrice Motsepe, wanda shi ma ya halarci filin wasa da ke Rabat, ya shaida faruwar abun inda ya nuna takaicin sa ga me da Eto’o.

A ranar Litinin hukumar gudanarwa ta nahiyar ta sanar da fara bincike kan “tashin hankali da kuma halayyar da ba a yarda da ita ba ta wasu ‘yan wasa da jami’ai” a wasannin ƙungiyoyi takwas na gasar ta AFCON.

A martanin da ta mayar, hukumar kwallon kafa ta Kamaru Fecafoot ta yi watsi da matakin na Caf, inda ta bayyana tsarin amatsayin abun shakku game da buƙatan shari’a mai adalci”.

Sannan Fecafoot ta nuna goyon bayanta ga shugabanta a cikin wata sanarwa a ranar Laraba, yayin da ta nuna cewa Eto’o zai daukaka kara kan hukuncin.

Tun bayan da ya hau kan mukaminsa a shekarar 2021, an lalata tasirin Eto’o a matsayin gwarzon wasan saboda wasu hayaniya da ke da alaka da badakala da matsaniya.

Inda ya fuskanci zarge-zargen rashin da’a da rashin kyakkyawan shugabanci, wasu masu ruwa da tsaki a kwallon kafa suma ke korafin manyan kura-kurai a cikin Fecafoot.

A yayin tantance ‘yan wasa da zasu wakilci Ƙasar Kamaru a gasar cin kofin kasashen Afirka da ke guda na a Moroko an zargi Eto’o da sanya baki wajan kawo sunayen wadda ya ke so yayin da ya ceri wadda ake ganin basa shiri irin su maitsaron ragar Manchester United Andrew Onana, da Vincent Abubakar.

Sai dai Eto’o ya sha musanta irin wadannan zarge-zargen, yana mai bayyana nasarorin da aka samu a matsayin shugaban Hukumar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Trump Ta Karawa Iran Wasu Takunkumai
Next Post: Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar Ya Shiga Jam’iyyar APC

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Kasashen Afirka Da Dama Suna Fafatawa Da Rasha A Yaki Da Ukraine Afrika
Anfara Samun Sakamakon Wucin Gadi a Kasar Guinea Conakry Labarai
Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran Afrika
Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai
INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi Labarai
Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
  • Hukumar Tsaron Teku A Libya Tafara Janye Jirgi Mai Dauke Da Iskar Gas Labarai
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda Najeriya
  • Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili Amurka
  • Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka
  • Rikici Ya Lafa A Kasar Iran Bayan Daukar Matakai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.