Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
Published: April 16, 2026 at 8:59 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jami’an Rundunar Karewa Al’umma a jihar Zamfara, da aka fi sani da “Askarawa”, sun kama wasu na’urorin fashewa, makudan kuɗaɗe, da sauran kayan tallafi da ake zargin za’a kaiwa ’yan bindiga a ƙauyen Bindin da ke Ƙaramar Hukumar Maru.

Kwamandan rundunar CPG na jihar, AIG Shehu Muhammad Dalijan (mai ritaya), ya bayyana hakan yayin da yake gabatar da waɗanda ake zargi tare da kayayyakin da aka ƙwato ga manema labarai a hedikwatar rundunar da ke Gusau.

Ya ce wannan nasara ta biyo bayan sahihan bayanan sirri da suka nuna cewa wata mota mai ɗauke da kaya ta tashi daga Danhasiya Plaza da ke Gusau zuwa ƙauyen Bindin, yankin da ake zargin yana ƙarƙashin ikon ’yan bindiga.

A cewarsa, jami’an sun tare motar mai lamba KMC 120-XR, inda suka kama direban tare da wasu mutane shida kuma ayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da kuɗi Naira miliyan 13,352,500, abubuwan fashewa 98 na na’urorin gargajiya (IEDs) da ake zargin dynamite ne, na’urorin tayar da fashewa guda 25, babura sababbi guda uku, wayoyin Android, sigari, ’ya’yan itacen tuffa, jarkoki huɗu na dizal, jarkoki uku na man ja, da kuma kayan haƙa kamar felaye da cokula.

Dalijan ya ce za a miƙa waɗanda aka kama tare da kayayyakin ga ’yan sanda domin ci gaba da bincike da kuma gurfanar da su a gaban kotu.

A cikin bayaninsa, direban motar, Abubakar Abdullahi Dangulbi, ya ce wani mai suna Aliyu Labaran ne ya ɗauke shi aiki domin kai kuɗin ga wani Alhaji Abubakar Bindin daga hannun wani Nasiru Dan Zuru (wanda ke tsere), yayin da aka ce na’urorin fashewar na wani Jamilu Lingyado ne a ƙauyen Bindin, Sai kuma yace bai san abin da ke cikin kayan ba, yana mai jaddada cewa shi aikin kai saƙo kawai aka ba shi.

“Ban san abin da ke cikin kayan ba. An ba ni aikin kai su ne kawai ga masu su a Bindin,” in ji shi.

Dalijan ya yi gargaɗi cewa matsalar tsaro da ke addabar jihar Zamfara na samun ƙarfi ne daga masu haɗin gwiwa da ke samar wa ’yan bindiga kayan aiki, bayanan sirri da sauran tallafi, ya kuma jaddada cewa irin waɗannan na’urorin fashewa na iya jawo asarar rayuka masu yawa ga fararen hula da jami’an tsaro.

Ya ƙara da cewa rundunar CPG za ta ci gaba da ƙara ƙaimi wajen yaƙi da masu aikata laifuka, tare da tabbatar da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin jihar.

Haka kuma, ya yaba wa gwamnatin jihar Zamfara kan tallafin kayan aiki da take bayarwa, yana mai cewa za a yi amfani da su yadda ya kamata wajen yaƙi da ’yan bindiga.

Wannan nasara ta ƙara nuna damuwa a tsakanin masana harkar tsaro cewa matsalar ’yan bindiga a Zamfara na ƙara samun goyon baya ta hanyar tsare-tsaren samar da kayayyaki masu ƙarfi, lamarin da ke buƙatar ƙarin tsauraran matakan sa ido da kuma katse hanyoyin samar da irin waɗannan kayayyaki.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
Next Post: Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Anyi Rashin Mutane Da Yawa Yayinda Bom Ya Fashe Ana Sallar Magariba Maiduguri Labarai
Wani Abu Ya Fashe A Asibitin Bagudo Dake Jihar Kebbi Tsaro
Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
Kasar Afirka Ta Kudu Ta Gayyaci Sabon Jakadan Amurka Afrika
Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya Ta Bawa Gwamnan Kebbi Mukamin Kyautata Harkar Kiwo Najeriya
Haryanzu Abubakar Malami Da Dansa Suna Hannun Hukumar EFCC Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Rasha Ta Nuna Kudurin Cimma Zaman Lafiya Da Ukraine Amurka
  • Kamfanin NNPC Yana Tattaunawa Da Wani Kamfanin Kasar China Labarai
  • Jamhuriyar Congo Zata Cigaba Da Fitar Da Ma’adanai Afrika
  • ‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka  Labarai
  • CAF Ta Ci Tarar Ƙasar Masar Dala 5,000 AFCON 2025 Wasanni
  • Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC Siyasa
  • Fafaroma Leo Zai Ziyarci Kasashen Afirka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.