Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaban Kasar Ghana Ya Soki Manufofin Gwamnatin Amurka
Published: March 25, 2026 at 4:34 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar talata a New York, shugaban kasar Ghana, John Daramani Mahama, ya soki manufofin gwamnatin Amurka, kan abunda ya kira amincewa da goge tarihin bakar fata, yana mai cewa hakan zai iya shafar wasu lamura sosai.

Tun bayan da ya dawo kan madafun iko, shugaba Donald Trump, ya auna hukumomi da cibiyoyin al’adun gargajiya, da suka hada da wuraren adana tarihi da wasu kayan al’adu, domin cire abunda ya kira “manufofin nuna kiyayya ga Amurka.”

Kalaman shugaba Trump da wasu dokokin shugaban kasa, da ake kira Executive orders, sun kai ga cire wasu kayan tarihin bautar da bakar fata, sake dawo da kayan tarihin turawa masu da’awar wariya, da wasu matakai da masu yakin tabbatar da ‘yancin tsiraru suke ganin zai maida hanun agogo baya.

Wadan nan matakai sun zama manhaja ga wasu gwamnatoci da kungiyoyi ko kamfanoni masu zaman kansu,” inji shugaba John Daramani, lokacin da yake magana a wani lamari a MDD, yace ko babu komi sannu a hankali matakan suna halatta goge tarihi.

Shugaba Mahama yace a Amurka ana cire kososhi da suke koyar da tarihin bakar fata a makarantu, ana tilastawa cibiyoyi su daina koyarda “gaskiyar tarhin bauta da wariyar launin fata,” kuma littatafai da suke karantar da wannan batu ana ci gaba da haramta su.

Shugaba Mahama a bara, ya amince da wani shirin karbar ‘yan asalin Afirka ta yamma da gwamnatin Trump ta tusa keyar su, a baya ya soki shugaba Trump kan karyar da yayi cewa ana yiwa turawa kisan kare dangi tare da kwache musu filaye a Afirka ta kudu, da cewa fadin hakan cin fuska ne ga daukacin Afirka.

Fadar White House bata maida martani nan take kan maganar shugaba John Daramani Mahama.

Afrika, Amurka, Labarai, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Dillalan Mai Suna Fuskantar Karancin Mai Sakamakon Yakin Amurka Da Iran
Next Post: Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70

Karin Labarai Masu Alaka

Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika
Sanyi Mai Tsanani Da Dusar Kankara Ya Tsaida Al’amura A Amurka Amurka
Jam’iyar APC A Najeriya Ta Kaddamar Da Bada Shaidar Zama Dan Jam’iyyar Ta Na’ura Mai Kwakwalwa Siyasa
Isra’ila Zata Mamaye Lebanon Labarai
Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20 Afrika
Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji A Kauyen Wanka Jihar Filato Afrika
  • Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka
  • Tsohon Shugaban Brazil Bolsanaro Zai Tafi Gidan Yari Labarai
  • Matatar Man Dangote Ta Samu Tagomashi Daga Abokan Hulda Najeriya
  • Tinubu: Sojojin Mu Sun Yi Rawar Gani Don Kare Demokuraɗiyya A Jamhuriyar Binin Labarai
  • Kasar Amurka Takara Saka Takunkumi Akan Kasar Venezuela Amurka
  • Ministan Harkokin Wajen Najeriya Yayi Murabus Afrika
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Gyara Dokar Kasafin Kudi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.