Tsohon lauyan Amurka Jack Smith wanda bai sami nasarar ci gaba da gurfanar da Trump gaban shari’a ba saboda zaben sa da aka yi, ya gayawa kwamitin majaisar wakilan Amurka ranar Alhamis cewa, Trump ya “nemi hanyoyin yin tazarce,” duk da cewa ya fadi zabe a shekara ta 2020, yayinda yake amsa zargen zargen da ‘yan Republican suke yi masa game da binciken da ya gudanar kan Donald Trump.
Jack Smith ya amsa tambayoyi daga kwamitin kula da harkokin shari’a karkashin ‘Yan Republican, kan kararraki biyu da ya shigar gaban kotu yana tuhumar Trump da laifin neman ci gaba da mulki alhali ya fadi zabe, da kuma murdiya kan muhimman kasidun gwamnati kana daga bisani yayi watsi da su bayan Trump ya sami nasara a zaben da aka yi bara.
Wannan shine karo na farko da Amurkawa za su ji daga bakin Smith kai tsaye kan wadannan shari’u biyu da suka mamaye harkokin Trump bayan ya sauka daga mulki.
“An tuhumi Trump ne saboda shaida ta tabbatar da gangan, ya karya dokokin da yasha rantsuwa zai kare,” Smith ya gayawa wakilan majalisa dake kwamitin. Ya ci gaba da cewa idan aka buka ce ni in jagoaranci shar’iar tsohon shugaban Amurka da shaidar da ake ita, zan yi haka ba tare da bata lokaci, ko la’akari daga wace jam’iyya ya fito ba.
Lauya Smith yace yana jin ma’aikatar shari’a ta Amurka zata shigar da kara a gaban kotu akansa, sakamkon binicken da yayi kan shugaba Trump.


