Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
  • Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika
  • NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027 Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya Afrika
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai

Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta
Published: March 23, 2026 at 1:56 PM | By: Bala Hassan

Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Bauchi ta yi Allah wadai da mummunan hari da wasu jami’an ‘yan sanda suka kai wa ma’aikatan gidan rediyon Albarka a Bununu, Tabawa Balewa LG, Jihar Bauchi a lokacin bikin Sallah.

“Wannan mummunan aiki na ta’addanci babban take hakkin dan adam ne, kuma ya zamo karan tsaye ga ‘yancin manema labarai, da kuma nuna rashin bin doka da oda daga jami’an da ake sa ran za su kare lafiya da dukiyoyin al’uma, ba cutar da ‘yan ƙasa ba.

Abin damuwa ne musamman ganin irin wannan rashin da’a yana faruwa a daidai lokacin da NUJ ke ƙara himma wajen fafutukar neman ƙwarewa da riƙon amana tsakanin hukumomin tsaro. ” inji ta.

Takardar dauke da sa hanun Sakataren ta na Jiha Isah Garba Gadau, an wallafa a ranar Litinin 23/03/2026
ta buƙaci Kwamishinan ‘Yan Sanda, na Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya gaggauta bincika lamarin tare da hukunta duk jami’in da aka sa me shi na da hannu a wannan mummunan aiki.

Bugu da ƙari, Ƙungiyar ta ce dole ne, ba tare da ɓata lokaci ba, Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Bauchi ta ɗauki alhakin biyan duk wani kuɗaɗen magani da wanda abin ya shafa ya kashe.

Idan kuma ba a cika waɗannan buƙatun ba, Ƙungiyar za ta kira taron gaggawa don yanke shawara kan mataki na gaba.

Ta kuma ƙara kira ga dukkan kafafen yaɗa labarai a jihar da su kasance cikin shiri kuma su jira ƙarin umarni domin Ƙungiyar ba za ta yi kasa a gwiwa ba har sai an yi adalci kuma an tabbatar da tsaron ‘yan jarida da kare musu mutuncinsu.

Ƙungiyar NUJ ba za ta lamunci cin zarafi, ko cin mutumcin ga ‘yan jarida a kowane hali ba.

In za’a iya tunawa a ranar lahadi 22 ga watan Maris 2026, kafan sadarwar zamani da kuma manyan gidajen jarida su ka wallafa hoton wani dan Jarida mai suna Muhammad Adamu ma’aikaci a gidan Rediyo Albarka da ke jihar Bauchi Arewa maso gabas a Najeriya cikin jini bayan da suka samu sa in sa tsakaninsa da Jami’in Dan Sanda mai kula da Division na Bununu da ke Karamar hukumar Tafawa Balewa Bauchi.

A cewar dan Jaridar ya je aiki ne dan dauko rahoton bukukuwar Sallah da ake yi a wannan gari ta Bununu, yayin da yazu shiga wajan sai DPOn ‘yan sanda na Bununu SP Jamilu Kabir da yaransa suka lakkada masa dukan kawo wuka har suka masa rauni a kansa ba tare da karya wata doka ba.

A bangaren ta rundunan ‘Yan Sanda na Jihar ta bakin Jami’in hulda da jama’anta SP Nafi’u Habib, ya ce sun samu labarin afkuwar lamarin suna kan bincike domin bin kadin duk mai gaskiya ta re da daukan matakin da ya dace a hukumance.

Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Ana Kokarin Dawo Da Wutan Lantarki A Cuba
Next Post: Shugaba Trump Yace Akwai Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Iran

Karin Labarai Masu Alaka

Yanayin Yunwa Yana Kara Ta’azarra A Somaliya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kotu Ta Bada Belin Abubakar Malami Bisa Wasu Sharruda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojojin Amurka Sunfara Isowa Gabas Ta Tsakiya Amurka
Guinea Bissau Ta Tsaida Gwaje-Gwajen Allurar Rigakafin Shawara A Kasar Labarai
Ministan Sadarwan Kasar Uganda Yayi Allah Wadai Da Kaiwa Bobi Wine Hari Afrika
Najeriya Zata Kara Mai Da Take Hakowa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato
  • Za’ayi Auren Zawarawa Dubu Uku A Kano
  • Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark
  • Matasa Sun Sayawa Ferfesa Pantami Fom Din Takarar Gwamnan Gombe
  • NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Na Duke Tsohon Ciniki Shirye-Shirye
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara Afrika
  • Shugaba Trump Yace Zai Dakatar Da Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran Afrika
  • Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe Afrika
  • An Garkame Dan Majalisa Watannin Takwas A Kasar Tunisiya Afrika
  • Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
  • Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
  • Gwamnatin Gombe: Babu Hannun mu a Cin Zarafin Kansilan Mazabar Shamaki Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.