A Burkina Faso, gwamnatin mulkin sojan kasar ta soke duka jam’iyun siyasar kasar, kamar yadda dokar mulkin soja da ake kira decree da majalisar ministocin kasar ta amince da ita ranar Alhamis.
Wannan shawara da shugabannin mulkin sojan kasar suka yanke bayan juyin mulkin da suka yi a shekara ta 2022, yana daga cikin matakai na baya-bayan nan da suka dauka na kara karfafa kama madafun iko a kasar.
Ministan harkokin cikin gidan kasar Emile Zerbo, yace binciken da gwamnati tayi ya nuna cewa yawan jam’iyun siyasa ya kara jawo rarrabuwar kawuna, tare da yin illa ga zamantake wa tsakanin jama’a.
Kamin juyin mulkin a kasar, Burkina Faso tana da jam’iyun siyasa samada dari daya, 15 daga cikin jam’iyun suna da wakilai a majalisar dokokin kasar.


