Yan bindiga sun hallaka mutane 162 a hare-hare da suka kai kauyuka a yammacin Nigeria, a cewar wani dan majalisa. Wannan na daga cikin hare-hare mafi muni a watanni baya-bayannan.
An kai harin ne kauyukan Woro da Nuku a jihar Kwara da daren ranar Talata, a cewar dan majalisa me wakiltar yankin, Muhammad Umar Bio.
Ya ce Lakurawa ne, kungiyar ‘yan ta’adda dake da alaka da ISIS ne suka kai harin. Ba wanda ya fito ya dau alhakin kai harin.


