Ranar talatar makon nan ne shugaban Amurka Donald Trump ya sanya hanu na kara wa’adin cinikayya tsakanin Amurka da kasashen Afirka ba tare da haraji ba da ake kira AGOA, na tsawon shekara daya, zuwa 31 ga watan Disamba shekara ta 2026.
Kara tsawon wa’adin ya kawo karshen zaman zullumi game da makomar shirin, yayinda kasashen duniya suke ji da matsanancin haraji da shugaban na Amurka ya azawa kasashen duniya ranar 2 ga watan Afrilun bara. Karewar wa’adin cinikayyar da ake kira AGOA ya jefa dubban ayyuka a nahiyar Afirka cikin hadari.
Kasar Lesotho, kasar Afirka da ta fi ko wacce dogaro kan kayayyaki da take sayarwa a kasuwannin Amurka, tsawaita wa’adin, ya sassauta zaman zullumi, ko da shike rashin tabbas din har yanzu yana nan.
“Ina da kwarin guiwar za’a sami wani abu na lokaci mai tsawo,” inji ministan harkokin kasuwanci na Lesotho Mokheti Shelile a hirar da yayi da kamfanin dillancin labarai na Reuters ofishinsa. Ya kara da cewa karin wa’adin na shekara daya bai dace da yanayin harkokin cinikayyar kasarsa ba. Bangaren sake-sake shine kan gaba na kayayyaki da Lesotho take sayarwa a kasashen ketare.
A watan Afrilun bara Amurka ta dorawa Lesotho harajin kashi 50 cikin dari, daga bisani gwamnatin Trump ta rage shi zuwa kashi 15 cikin dari, duk da haka wannan harajin yana da nauyi ga Lesotho wacce ta dogara kan cinikin kayayyakin sawa da Amurkawa suke saye.


