Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran
Published: March 25, 2026 at 3:40 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: March 25, 2026

Prime Ministan Pakistan Shebbaz Shariff, ya fada ranar talata cewa a shirye yake ya zama mai masaukin baki a shawarwari tsakanin Amurka da Iran na kawo karshen yakin na yankin Gulf, kwana daya bayan da shugaban Amurka Donald Trump, ya dakatar da barazanar da yayi na kai hari kan cibiyoyin wutan lantarki na Iran, cewa an gudanar da shawarwari masu ma’ana.

Duk da haka, Amurka tana shirin tura dubban karin sojoji daga runduna ta 82 zuwa gabas ta tsakiya, kamar yadda mutane biyu da suke da masaniya dangane da batun suka shaidawa kamfanin dillancn labarai na Reuters. Kari kan tulin dakarun da ta aike yankin, wadda hakan yake kara janyo fargabar yakin zai dauki lokaci mai tsawo.

A rubutu da ya wallafa a shafin dandalin sada zumunta na X, PM Sharif yace, Pakistan tana maraba, kuma tana bada cikakken goyon baya kan kokari da ake yi na yin shawarwari domin kawo karshen yakin.

Ahalinda ake ciki kuma, rahotanni suka ce Iran ta tsananta matsayinta kan shawarwarin yayinda tayi ruwan makamai masu linzami kan Isra’ila, kasuwar hannayen jari a Amurka ta fadi kasa, saboda fargabar babu alamar kakkautawa a rikicin da ake yi a yankin.

A wata kuri’ar neman jin ra’ayin jama’a da kamfanin dillancin labarai na Reuters da IPSOS, suka gudanar, ya nuna farin jinin shugaban Amurka Donald Trump ya zube zuwa kashi 36 cikin dari matsaya mafi karanci tunda ya koma fadar White House, saboda karin farashin mai.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Eberechi Eze Ba Zai Buga Wasannin Da Ingila Za Tayiba Arteta
Next Post: Isra’ila Zata Mamaye Lebanon

Karin Labarai Masu Alaka

Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
Wasu Yara 50 Sun Kubuta Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai
Shugaban Kasar Koriya Ta Arewa Ya Zamo Sakataren Jam’iya Mai Mulki Labarai
Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci Afrika
EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
Hawan Sallah A Jihar Katsina Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

https://www.youtube.com/watch?v=sainfSmn-EQ

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • “Banga Abun Da Zai Canza Ba A Nadin Janar Christopher Ministan Tsaro” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
  • Pakistan Zata Karbi Tattaunawar Rikicin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika
  • Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.