Ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Ikeja a jihar Legas, James Faleke, ya karɓi fom ɗin na gani Ina so da na tsayawa takara na jam’iyyar APC a madadin Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu gabanin zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.

Majiyoyi sun rawaito cewa, sakataren tsare-tsare na ƙasa na APC, Suleiman Argungu, ne ya bayyana fara wannan tsari na siyar da fom a ranar Talata a Abuja, inda ya miƙa fom ɗin ga Faleke, wanda kuma shi ne wanda ya kafa ƙungiyoyin goyon bayan Tinubu.
Rahotanni sun nuna cewa Faleke ya biya kuɗin fom ɗin da ya kai naira miliyan 100 a madadin shugaban ƙasar, abin da ke nuna fara shirye-shiryen neman sake zaɓen Tinubu a hukumance.
Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa, INEC, ta tsara gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na majalisar tarayya a ranar Asabar, 16 ga Janairu, 2027, yayin da zaɓen gwamna da na majalisun jihohi za su gudana a ranar 6 ga Fabrairu, 2027.
Haka kuma, hukumar ta sanar da cewa za a gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyyun siyasa daga ranar 23 ga Afrilu, 2026 zuwa 30 ga Mayu, 2026, tare da warware duk wata takaddama da ka iya tasowa a wannan lokaci.
INEC ta kuma bayyana cewa yaƙin neman zaɓe na shugabancin ƙasa da na majalisar tarayya zai fara ne daga ranar 19 ga Agusta, 2026, yayin da na gwamna da na majalisun jihohi zai fara daga ranar 9 ga Satumba, 2026.
Ana sa ran ƙarin bayani zai biyo baya kan wannan lamari.


