Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar NAHCON Fitar Da Jadawalin Fara Jigilar Alhazain Najeriya Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya Afrika
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai

Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa
Published: April 28, 2026 at 2:28 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Ikeja a jihar Legas, James Faleke, ya karɓi fom ɗin na gani Ina so da na tsayawa takara na jam’iyyar APC a madadin Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu gabanin zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.

Majiyoyi sun rawaito cewa, sakataren tsare-tsare na ƙasa na APC, Suleiman Argungu, ne ya bayyana fara wannan tsari na siyar da fom a ranar Talata a Abuja, inda ya miƙa fom ɗin ga Faleke, wanda kuma shi ne wanda ya kafa ƙungiyoyin goyon bayan Tinubu.

Rahotanni sun nuna cewa Faleke ya biya kuɗin fom ɗin da ya kai naira miliyan 100 a madadin shugaban ƙasar, abin da ke nuna fara shirye-shiryen neman sake zaɓen Tinubu a hukumance.

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa, INEC, ta tsara gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na majalisar tarayya a ranar Asabar, 16 ga Janairu, 2027, yayin da zaɓen gwamna da na majalisun jihohi za su gudana a ranar 6 ga Fabrairu, 2027.

Haka kuma, hukumar ta sanar da cewa za a gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyyun siyasa daga ranar 23 ga Afrilu, 2026 zuwa 30 ga Mayu, 2026, tare da warware duk wata takaddama da ka iya tasowa a wannan lokaci.

INEC ta kuma bayyana cewa yaƙin neman zaɓe na shugabancin ƙasa da na majalisar tarayya zai fara ne daga ranar 19 ga Agusta, 2026, yayin da na gwamna da na majalisun jihohi zai fara daga ranar 9 ga Satumba, 2026.

Ana sa ran ƙarin bayani zai biyo baya kan wannan lamari.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya
Next Post: Hukumar NAHCON Fitar Da Jadawalin Fara Jigilar Alhazain Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Za A Rantsar Da Mainasara Kogo A Matsayin Shugaban Kundin Da’ar Ma’aikata Labarai
Prime Ministan Senegal Ya Bayyana Shirin Sauya Sheka Afrika
Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Roger Lumbala Shekaru 30 Labarai
‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka
Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya Afrika
Kamfanin Hakar Ma’adanai Na Kasar Kanada Ya Cigaban Da Aikinsa Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Matasa Sun Sayawa Ferfesa Pantami Fom Din Takarar Gwamnan Gombe
  • Hukumar NAHCON Fitar Da Jadawalin Fara Jigilar Alhazain Najeriya
  • Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya
  • UNICEF Ta Tallafawa Jihar Bauchi Da Babura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Karamar Sallah: Hukumar Kashe Gobara A Gombe Ta Kuduri Aniyar Kare Al’umma Afrika
  • Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
  • Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ukraine Ta Mika Wa Amurka Daftarin Yarjejeniya Da Rasha Sauran Duniya
  • Rasha Ta Yiwa Amurka Tayin Daina Bada Bayanan Sirri Afrika
  • Burkina Faso: Mun Kama Sojojin Najeriya da Jirgin Yaki Bisa Shigowa Ba Bisa Ka’ida Ba Afrika
  • Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro
  • Gwamnatin Jihar Yobe: Ana Cin Zarafin Fursunoni A Gidan Gyaran Halin Potiskum Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.