Shugaban Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka A Afirka Yace Akwai Rashin Fahimta A Tsakanin Kasashen Da Amurka Take Tallafawa
Akwai manyan batutuwa ko rashin fahimta dake kunno kai a yarjejeniyar kiwon lafiya da Amurka take kullawa da kasashen Afirka dangane da yadda tallafin kudi da Amurka take bayarwa zai rika aiki daga yanzu, kamar yadda shugaban hukumar sa ido da hana yaduwar cututtuka a Afirka ya fada ranar Alhamis. “Akwai damuwa sosai game da…

