Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa
Published: December 11, 2025 at 7:56 AM | By: Bala Hassan | Updated: December 18, 2025

Ceto ɗaliban Neja ya dawo da natsuwa ga ƙasa, inji Ministan Yaɗa Labarai.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris ya ce ceto ɗaliban da aka sace daga Makarantar Firamare da Sakandare ta St. Mary da ke Papyri, Jihar Neja, ya dawo da natsuwa da kwanciyar hankali ga iyalan su da ƙasa baki ɗaya.

Ministan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba lokacin da ya jagoranci tawagar Gwamnatin Tarayya zuwa Fadar Gwamnatin Jihar Neja domin yin godiya da kuma bayyana jin daɗin dawowar yaran lafiya.

 

 

 

 

 

 

Tawagar ta samu tarbar Gwamnan Jihar Neja, Umaru Mohammed Bago.

Idris ya jaddada cewa haɗin kai tsakanin jami’an tsaro, Gwamnatin Jihar Neja da al’ummar yankin ne ya taimaka wajen nasarar aikin ceton.

Ya ce: “Ceton waɗannan yara ya dawo da natsuwa ga iyalan su da kuma ga ƙasa baki ɗaya. Mun yaba da jajircewar jami’an tsaro, saurin ɗaukar matakin Gwamnatin Jihar Neja, da kuma haɗin kan al’umma wanda ya ba da damar samun wannan sakamakon.”

Ministan ya kuma jaddada cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta ɗauki tsaron makarantu da kare ɗalibai da matuƙar muhimmanci.

Ya ƙara da cewa, “Dole ’ya’yan mu su samu damar yin karatu cikin tsaro. Gwamnatin Tarayya tana da cikakkiyar niyyar ci gaba da aiki tare da jihohi domin ƙarfafa tsaron makarantu, tare da tabbatar da cewa irin wannan ɓarna ga zaman lafiyar mu bai da wurin zama a ƙasar mu.”

A jawabin sa, Gwamna Bago ya gode wa Ministan bisa ziyarar, tare da yaba wa jami’an tsaro da al’ummomin yankin waɗanda suka taka rawa wajen ganin an sako ɗaliban.

Ya kuma jaddada cewa jihar za ta ci gaba da aiki tare da Gwamnatin Tarayya domin ƙarfafa tsaro da zaman lafiya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya
Next Post: Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026

Karin Labarai Masu Alaka

Mayakan Houthi Zasu Shiga Yakin Amurka Da Isra’ila Afrika
‘Yan Bindiga A Mali Sun Kashe Direbobin Manyan Motoci Afrika
Prime Ministar Italiya Ta Ziyarci Saudi Arabia Afrika
Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba Labarai
Rasha Ta Gargadi Amurka Da Isra’ila Kan Harin Iran Afrika
Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Arsenal Tana Ci Gaba Da Kokarin Dauko Morgan Rogers Wasanni
  • Iran Da Amurka Zasu Kulla Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
  • Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
  • Wike: Bazamuyi Sake Fubara Ya Sake Samun Nasara Ba Najeriya
  • Kwamitin Aikin Hajjin Najeriya Ya Shigar Da Korafi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumar NAHCON Ta Bude Asibiti A Madina Afrika
  • Shugaban Amurka Donald Trump Ya Jadda da Kudirinsa Da Kwace Iyakar Greenland Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.