Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna Afrika
  • Tinubu Ya Buƙaci Musulmi Su Riƙe Haƙuri, Tawali’u Da Tausayi Afrika
  • Maulidin 2026: IMC Ta Yi Kira Da Ƙarfafa Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Najeriya Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai Afrika
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika

Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa
Published: December 11, 2025 at 7:56 AM | By: Bala Hassan | Updated: December 18, 2025

Ceto ɗaliban Neja ya dawo da natsuwa ga ƙasa, inji Ministan Yaɗa Labarai.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris ya ce ceto ɗaliban da aka sace daga Makarantar Firamare da Sakandare ta St. Mary da ke Papyri, Jihar Neja, ya dawo da natsuwa da kwanciyar hankali ga iyalan su da ƙasa baki ɗaya.

Ministan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba lokacin da ya jagoranci tawagar Gwamnatin Tarayya zuwa Fadar Gwamnatin Jihar Neja domin yin godiya da kuma bayyana jin daɗin dawowar yaran lafiya.

 

 

 

 

 

 

Tawagar ta samu tarbar Gwamnan Jihar Neja, Umaru Mohammed Bago.

Idris ya jaddada cewa haɗin kai tsakanin jami’an tsaro, Gwamnatin Jihar Neja da al’ummar yankin ne ya taimaka wajen nasarar aikin ceton.

Ya ce: “Ceton waɗannan yara ya dawo da natsuwa ga iyalan su da kuma ga ƙasa baki ɗaya. Mun yaba da jajircewar jami’an tsaro, saurin ɗaukar matakin Gwamnatin Jihar Neja, da kuma haɗin kan al’umma wanda ya ba da damar samun wannan sakamakon.”

Ministan ya kuma jaddada cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta ɗauki tsaron makarantu da kare ɗalibai da matuƙar muhimmanci.

Ya ƙara da cewa, “Dole ’ya’yan mu su samu damar yin karatu cikin tsaro. Gwamnatin Tarayya tana da cikakkiyar niyyar ci gaba da aiki tare da jihohi domin ƙarfafa tsaron makarantu, tare da tabbatar da cewa irin wannan ɓarna ga zaman lafiyar mu bai da wurin zama a ƙasar mu.”

A jawabin sa, Gwamna Bago ya gode wa Ministan bisa ziyarar, tare da yaba wa jami’an tsaro da al’ummomin yankin waɗanda suka taka rawa wajen ganin an sako ɗaliban.

Ya kuma jaddada cewa jihar za ta ci gaba da aiki tare da Gwamnatin Tarayya domin ƙarfafa tsaro da zaman lafiya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya
Next Post: Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026

Karin Labarai Masu Alaka

Dakarun Sakai A Kasar Sudan Sun Kashe Mutane 28 A Wani Farmaki Afrika
APC Ta Bayyana Abba Yusuf A Matsayin Halastaccen Ɗan Takara Bayan Cika Sharudda Afrika
Jakadan Amurka A Poland Ya Yanke Hulda Da Kakakin Majalisar Kasar Labarai
Iran Tace Dole A Tsagaita Wuta A Lebanon Kafun Fara Shawarwari Amurka
Masu Hakar Ma’adanai 37 Sun Mutu A Jihar Filato Bidiyo
Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Fanny Amun Ya Yi Murabus A Matsayin Shugaban Kwamitin Binciken NFF
  • Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna
  • Tinubu Ya Buƙaci Musulmi Su Riƙe Haƙuri, Tawali’u Da Tausayi
  • Ceferin Ya Ce Ba Zai Yi Takarar Shugabancin FIFA Ba
  • Maulidin 2026: IMC Ta Yi Kira Da Ƙarfafa Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Najeriya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa Amurka
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
  • Shugabannin Darikar Anglican Sun Bada Sanarwar Kafa Sabuwar Majalisa Afrika
  • Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot. Wasanni
  • Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar Labarai
  • Ankara Kai Wani Harin Bom Birnin Maiduguri Afrika
  • Tantance Gaskiyar Bayanai Shi Ne Ginshiƙin Aikin Jarida Mai Nagarta – Abdulaziz Afrika
  • Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026 Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.