Kwamitin Gudanarwar Hukumar Hajji ta Najeriya Ya Shigar da Ƙorafi ga Tinubu, Ya Nemi A Sauke Shugaban Hukumar Bisa Zargin Cin Hanci da Rashawa
Mambobin kwamitin gudanarwa na Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) sun rubuta wa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu wasiƙa, suna neman a sauke shugaban hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Usman (Pakistan), bisa zargin cin hanci da rashawa, rashin ƙwarewa da cin zarafin mukami.
Wasiƙar, mai kwanan wata 19 ga Janairu, 2026, ta nuna cewa zarge-zargen sun haɗa da kashe kuɗaɗe ba tare da amincewar kwamitin ba, bayar da kwangiloli ba tare da bin dokokin BPP ba, da kuma karya ƙa’idojin tafiyar da harkokin kuɗi. Kwamitin ya kuma ce shugaban yana ƙarƙashin binciken EFCC.
Mambobin sun ce waɗannan matsaloli sun janyo raguwar amincewa da hukumar, tare da haifar da rashin jituwa da Masarautar Saudiyya, wanda hakan ya sa aka rage yawan maniyyatan Najeriya daga 95,000 a 2025 zuwa 50,000 a Hajjin 2026.
Kwamitin ya bayyana cewa ci gaba da barin Farfesa Usman a mukami na iya kawo cikas ga shirye-shiryen Hajji mai zuwa, tare da jefa Najeriya cikin haɗarin aiki da diflomasiyya.
Ƙoƙarin jin ta bakin sa ya ci tura, sai dai a baya ya ce koke-koken da ake yi a kansa suna da nasaba da hassada a cikin hukumar.


