Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kwamitin Aikin Hajjin Najeriya Ya Shigar Da Korafi
Published: January 22, 2026 at 11:33 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 22, 2026

Kwamitin Gudanarwar Hukumar Hajji ta Najeriya Ya Shigar da Ƙorafi ga Tinubu, Ya Nemi A Sauke Shugaban Hukumar Bisa Zargin Cin Hanci da Rashawa

Mambobin kwamitin gudanarwa na Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) sun rubuta wa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu wasiƙa, suna neman a sauke shugaban hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Usman (Pakistan), bisa zargin cin hanci da rashawa, rashin ƙwarewa da cin zarafin mukami.

Wasiƙar, mai kwanan wata 19 ga Janairu, 2026, ta nuna cewa zarge-zargen sun haɗa da kashe kuɗaɗe ba tare da amincewar kwamitin ba, bayar da kwangiloli ba tare da bin dokokin BPP ba, da kuma karya ƙa’idojin tafiyar da harkokin kuɗi. Kwamitin ya kuma ce shugaban yana ƙarƙashin binciken EFCC.

Mambobin sun ce waɗannan matsaloli sun janyo raguwar amincewa da hukumar, tare da haifar da rashin jituwa da Masarautar Saudiyya, wanda hakan ya sa aka rage yawan maniyyatan Najeriya daga 95,000 a 2025 zuwa 50,000 a Hajjin 2026.

Kwamitin ya bayyana cewa ci gaba da barin Farfesa Usman a mukami na iya kawo cikas ga shirye-shiryen Hajji mai zuwa, tare da jefa Najeriya cikin haɗarin aiki da diflomasiyya.

Ƙoƙarin jin ta bakin sa ya ci tura, sai dai a baya ya ce koke-koken da ake yi a kansa suna da nasaba da hassada a cikin hukumar.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Kasar China Ta Daina Bada Bashi Da Dalar Amurka Sai Da Kudin Kasar Yuan
Next Post: Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar-Ta-Baci A Fannin Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Musa: “Da Yaddar Allah Zamu Ga Bayan Ta’addanci A Najeriya” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata Labarai
  • ECOWAS Zata Kafa Rundunar Yaki Da Rashin Tsaro Afrika
  • Rasha Takai Sabbin Hare-Hare Akan Wasu Biranen Ukraine Tsaro
  • Wani Abu Ya Fashe A Ofishin Jakadancin Amurka Dake Kasar Norway Afrika
  • Amurka Ta Kwace Jirgin Mai Mallakar Rasha Amurka
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.