Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Kwamitin Ardo Chindo Ya Buƙaci A Hana Mamaye Filayen Kiwo da Gandun Daji
Published: July 28, 2026 at 4:26 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kwamitin Aiwatar da Fararen Takardar Kula da Filayen Kiwo a Jihar Gombe, ƙarƙashin jagorancin Dakta Ardo Chindo Abubakar, ya kai ziyarar aiki zuwa Masarautun Billiri da Pindiga domin ci gaba da wayar da kan al’umma da kuma tabbatar da aiwatar da manufofin gwamnati na samar da zaman lafiya tsakanin makiyaya da manoma.

A lokacin ziyarar a Billiri, Shugabar Ƙaramar Hukumar Billiri, Hajiya Eglah Idris, ta tarbi mambobin kwamitin tare da tabbatar musu da cikakken goyon baya da haɗin kai wajen sauke nauyin da aka ɗora musu.

Ta roƙi kwamitin da ya yi la’akari da bai wa manoman da suka riga suka noma a cikin filayen kiwo damar girbe amfanin gonakinsu na bana kafin a fara cikakken aiwatar da dokokin, bisa amincewar hakimai da shugabannin ƙauyuka.

Da yake mayar da martani, Shugaban Kwamitin, Dakta Ardo Chindo Abubakar, tare da Daraktan Gandun Daji na Jihar Gombe, Alhaji Musa Suleiman Kumo, sun bayyana cewa wannan shawara abin maraba ne, tare da alƙawarin yin nazari a kanta yayin aiwatar da matakan gwamnati.

Dakta Ardo Chindo ya bayyana cewa kwamitin ya fuskanci ƙalubale a wasu sassan jihar sakamakon rikice-rikicen da ke faruwa tsakanin makiyaya da manoma, amma ya jaddada aniyarsa ta ƙara ƙaimi wajen tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa.

A Masarautar Pindiga kuwa, Hakimin Garin Galadima, Alhaji Muhammad Kawuwa Ahmad, ya ce a wasu lokuta hukumomin gargajiya ba sa samun bayanan wasu matsaloli tun da wuri, lamarin da ke haddasa ta’azzarar rikice-rikice.

Hakimin ya buƙaci al’umma su ci gaba da zaman lafiya da juna tare da mara wa manufofi da shirye-shiryen gwamnati baya domin samun ci gaba.

Shi ma Shugaban Hukumar Raya Karkara ta Pindiga (LCDA), Alhaji Garba Yakubu, Walin Pindiga, ya yaba wa gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya bisa samar da yanayi na zaman lafiya da inganta rayuwar al’ummar jihar.

Ya kuma tabbatar wa kwamitin da cikakken goyon baya wajen aiwatar da shawarwarin Farar Takarda domin samar da mafita mai ɗorewa ga rikice-rikicen makiyaya da manoma.

A nasa jawabin, Hakimin Kolmani, Barrista Muhammad Magaji Ibrahim, ya buƙaci a ɗauki tsauraran matakai kan duk masu mamaye filayen kiwo da gandun daji ba bisa ƙa’ida ba.

Ya ce duk wanda aka samu da laifin sayar da filayen kiwo ko hanyoyin shanun gwamnati ya kamata a hukunta shi bisa tanadin doka domin hana sake aukuwar irin wannan matsala.

Har ila yau, Daraktan Gandun Daji, Alhaji Musa Suleiman Kumo, ya yi kira ga masu sare bishiyoyi ba tare da izini ba da su daina wannan danyen aiki, yana mai buƙatar al’ummar jihar su kasance masu bin doka tare da bai wa gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya cikakken haɗin kai wajen tabbatar da ci gaba mai ɗorewa da zaman lafiya a jihar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gidauniyar Jalo Wali Ta Ƙaddamar Da Bada Audugar Mata A Gombe
Next Post: Haɗin Gwiwar GOSERC Da Savannah Zai Ƙarfafa Rarraba Wutar Lantarki A Faɗin Jihar Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi Afrika
INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya
Shugabannin Darikar Anglican Sun Bada Sanarwar Kafa Sabuwar Majalisa Afrika
Fiye Da Mutane Miliyan Hudu Suna Fuskantar Barazanar Yunwa A Somaliya Sauran Duniya
Hukumar Ƴan Sanda Ta Musanta Zargin Kashe Ɗan Achaba a Gombe Tsaro
Sallah Sai Ranar Juma’a A Najeriya: Fadar Sarkin Musulmi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sabon Magajin Garin New York Zai Soke Wasu Dokoki Amurka
  • Hukumar Tsaron Teku A Libya Tafara Janye Jirgi Mai Dauke Da Iskar Gas Labarai
  • ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
  • Shirin: Lafiya Jari Ce 11.21.25 Kiwon Lafiya
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamna Abba Ya Gana Da Kwankwaso Kamun Ganawarsa Da Tinubu Siyasa
  • Harin Da Israela Ta Kai Gaza Yayi Ajalin Mutane 27 Da Yara Uku Labarai
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.