Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025
Published: November 30, 2025 at 7:44 AM | By: Bala Hassan | Updated: November 30, 2025

JIHAR NASARAWA TA ƊAUKI KYAUTAR KWALLON KAFAR KURAME.

Ƙungiyar Kwallon Kafa na Kurame Deaf, ta jihar Nasarawa a Tarayyar Najeriya ta lashe kofin gasar a bana.

Gasar wadda ta ƙunshi jihohi goma, ciki har da Nasarawa, Rivers, Niger, Kaduna, Kano, Kebbi, da masu masaukin baki, Plateau, Adamawa, Bauchi, da FCT, Abuja, ta fara ne a ranar 19 ga Nuwamba, 2025, a cibiyoyi daban-daban a Jos, Jihar Plateau.

Sakatariyar Wasanni ta Musamman na Jihar Nasarawa, Ms Patricia David Oshuwayine, ita ta wakilci Ma’aikatar Matasa da Ci gaban Wasanni ta Jihar Nasarawa a gasar.

Kwamishinan Ci gaban Matasa da Wasanni na Jihar Nasarawa, Hon. Kwanta Yakubu, ya taya Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Kurame na Jihar murna nasarar da suka samu a gasar cin kofin ƙwallon ƙafa ta ƙasa ta karo na 6 da aka gudanar a Jos, Jihar Plateau.

Kwanta ya ce, “Makonni kaɗan da suka gabata, na haɗu da membobin ƙungiyar a sansaninsu da ke Lafia, kafin fara gasar, kuma na ƙarfafa musu gwiwa don su yi duk mai yiwuwa don faranta wa Gwamna Abdullahi Sule da Jihar rai ta hanyar lashe gasar a Jos, kuma zan gabatar da su ga Gwamna.

“A yau, Gwamna Abdullahi Sule da dukkan al’umar Jihar suna alfahari da rawar da ƙungiyar ta taka.

“‘Yan wasanmu masu hazaka sun fafata da manyan ƙungiyoyi daga ko’ina cikin ƙasar, kuma daga ƙarshe sun yi nasara

“Muna yi wa sabbin zakarun ƙasa alƙawarin tarba mai kyau da kuma shirya ya musu liyafa ta musamman a Lafia, Babban Birnin Jiha,” in ji Kwamishinan.

Tawagar ƙungiyar Nasarawa ta samu wannan nasararne bayan da ta doke tawagar ƙungiyar kwallon kafa ta Kurame na Jihar Kaduna da ci 1-0 a ranar Asabar 29 ga watan Nuwamban 2025.

Da yake zantawa da yan jarida mai horas da ƙungiyar na jihar Nasarawa Jafar Umar yace kafin lashe wannan gasar ta wagar Nasarawa ta doke masu ma saukin baki jihar Plateau,Adamawa,Kebbi,da jihar Niger.

Kamar yadda Jami’in hulda da jama’a na Ma’aikatar Matasa da Ci gaban Wasanni na Jihar Nasarawa, Eche Amos ya fitar a wata ta karda da ya rabawa mane ma labarai.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba!
Next Post: Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce!

Karin Labarai Masu Alaka

Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz Wasanni
Da Alamu Ronaldo Zai Buga Dukkan Wasanni Da Gasar Kofin Duniya A 2026 Wasanni
Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
FIFA, Ta Tabbatar Da Ranar Mika Sunayen ‘Yan Wasa AFCON 2025. Wasanni
Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas Najeriya
  • Ga Dukkan Alamu Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Bai Kare Ba Sauran Duniya
  • Gwamnatin Janhuriyar Nijar Ta Soke Lasisin Wasu Kamfanonin Dakon Mai Afrika
  • Kudaden Shigan Kasar Namibia Ya Bunkasa Saboda Tashin Farashin Gwal Labarai
  • Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza Labarai
  • Marc Brys: “Eto’o Baiyi Adalci Ga Onana, Da Vincent, Ba” Wasanni
  • Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.