Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar
Published: March 26, 2026 at 6:19 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, na gaggauta kokarin amincewa da kasafin kudin ƙasa domin kauce wa zabukan wuri-wuri da ake ganin zai iya sha kaye a cikinsu, yayin da yakin da ake yi da Iran bai kawo wani gagarumin sauyi a yadda ake kallonsa a kuri’un jin ra’ayin jama’a ba.

A kwanakin farko na yakin, bangaren Netanyahu ya ga wata dama ga kawancen jam’iyyunsa na dama su amfana da harin farko da ya kashe Ayatollah Ali Khamenei, ta hanyar gudanar da zabuka kafin lokacin da ake sa ran yi a watan Oktoba, kamar yadda wata majiya mai masaniya kan dabarun siyasarsa ta bayyana.

Daya daga cikin hanyoyin tilasta gudanar da zabukan gaggawa ita ce a bar majalisar dokoki ta kasa amincewa da kasafin kudin kafin ranar 31 ga Maris, wanda a karkashin dokar Isra’ila zai jawo gudanar da zabe cikin kwanaki 90. Yayin da hare-haren hadin gwiwar Amurka da Isra’ila suka kashe manyan jami’an Iran da dama, wasu na kusa da Netanyahu sun fito fili suna hasashen yiwuwar gudanar da zabe a watan Yuni.

Sai dai kusan makonni hudu da fara yakin, wanda har yanzu bai cimma daya daga cikin manyan manufofinsa na kifar da gwamnatin malaman addini ta Iran ba, firaministan Isra’ila mafi dadewa a mulki na kokarin kauce wa zabukan wuri-wuri, kamar yadda mambobi uku na gwamnatinsa suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

Afrika, Labarai, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji A Jihar Kebbi
Next Post: Ma’aikatar Tsaron Amurka Zata Kara Samar Da Makamai

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Samun Sakamako Mai Kyau A Tattaunawa Da Amurka Amurka
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar Afrika
Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak Labarai
Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC Afrika
Shugaban Kasar Uganda Yana Kokarin Mayar Da Mulkin Kasar Na Gado Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus
  • Hukumar ‘Yan Sanda Sun Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe
  • Kasar Congo Ta Kawo Karshen Cutar Kyandar Biri
  • Mutane 15 Sun Rasa Rayukan Su A Gabashin Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kwango
  • Kungiyoyi Sunyi Kasashen Jinkiri A Bunkasar Tattalin Arzikin Kashen Afirka

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya Labarai
  • Kasar Malawi Ta Kaddamar Da Rigakafin Shan Inna Kiwon Lafiya
  • Musa: “Da Yaddar Allah Zamu Ga Bayan Ta’addanci A Najeriya” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Guinea An Zabi Madugun Sojojin Da Suka yi Juyin Mulki Mamady A Shugaban Ƙasar, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran Afrika
  • Ƙungiyoyin Premier 17 Za Su Rasa ‘Yan Wasa 40 saboda Gasar AFCON 2025, Wasanni
  • Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.