Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya
Published: March 11, 2026 at 4:29 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Da yai magana kan rikicin na gabas ta tsakiya, shugaban majalisar tarayyar turai, Antonio Costa, ya fada ranar talata cewa Rasha ce take cin ribar yakin da ake yi a gabas ta tsakiya, ganin farashin mai ya tashi, kuma ya kauda hankali daga yakin da take da Ukraine.

“Zuwa yanzu dai kasa daya ce ta sami nasarar wannan yaki,” itace Rasha, Costa ya fada a wani jawabi da yayi wa jakadun Kungiyar tarayyar turai.

Antonio Costa, ya jaddada bukatar kungiyar tarayyar turai ta kare tsarin duniya na bin doka da oda, wadda yace ahalin yanzu Amurka take yi wa kalubale, daga nan ya shawarwaci duka sassa a rikicin na gabas ta tsakiyya, su koma teburin shawarwari.

Ahalinda ake ciki kuma, farashin mai ya fadi da kamar kashi 15 cikin dari ranar talata, kwana daya bayanda mai yayi tashin goron zabbi, rabon da ya kai haka tun 2022, faduwar farashin ya biyo bayan kalaman shugaban Amurka Trump cewa yakin ya kusa zuwa karshe.

Yau mai da ake kira Brent ana cinikinsa kan dala 84 da centi 73 kan ko wani gangar danyen mai, yayinda wadda ake kira West Texas shi kuma ya tashi kan dala 80 da centi 31. Farashin ya kara faduwa, bayan da ministan makamashi na Amurka Chris Wright ya rubuta a shafinsa na X cewa, sojojin Amurka sun taimaka an wuce da mai ta mashigan ruwa na Hormuz.

Wannan lamari na tsadar mai yana kalubale ga rinjayen da jam’iyyar Republican take dashi a zaben rabin wa’adi mai zuwa, kamar dai yadda masu nazarin harkokin yau da kullum suke hasashe.

Har yanzu dai kan yakin na gabas ta tsakiya, Australia zata tura jirgin leken asiri zuwa gabas ta tsakiya, kuma zata aike da makamai masu linzami zuwa hadaddiyar daular larabawa, amma ba zata tura sojojinta na kasa zuwa Iran ba, PM kasar Anthony Albanese ya fada a ranar talata.

Albanese yace, taimakon da Australia take da kayan yaki, zai taimakawa kasashe da suke yankin Gulf su kare kan su daga hare hare daga Iran ba babu hujja.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran
Next Post: Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71 Labarai
Netanyahu: Zamu Kashe Dala Billiyan $110 Cikin Shekaru Hudu Don Kera Makamai Sauran Duniya
Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal Afrika
Bankin Duniya Zaibawa Kasar Mozambique Lamunin Dala Bilyan Shida Labarai
‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji A Kauyen Wanka Jihar Filato Afrika
Ministan Sadarwan Kasar Uganda Yayi Allah Wadai Da Kaiwa Bobi Wine Hari Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugabannin Kasashen Afirka Ta Tsakiya Sun Kamallah Taron Koli Afrika
  • An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Talata 11.18.2025 Rediyo
  • Sakataren Harkokin Wajen Amurka Yace Rahoton Kasashe Biyar Akan Rasha Yana Dauke Da Damuwa Amurka
  • ECOWAS Ta Saka Dokar Ta Baci A Afrika Ta Yamma Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda Najeriya
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000 Najeriya
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.