Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa
Published: January 22, 2026 at 7:45 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 22, 2026

A halin da ake ciki, Kasar Spain ta yi kira ga Tarayyar Turai da ta dauki matakan kirkiro rundunar sojojin hadin guiwa ta Kasashen Tarayyar Turai, domin ta zamo hannunka mai sanda ga duk wani mai neman nuna musu yatsa.

Ministan harkokin wajen Spain, Jose Manuel Albares ya fada ranar laraba cewa ya kamata kasashen Turai su fara da hada hancin kayan tsaron da suke da su da hade masana’antunsu na tsaro, kafin su kafa runduna guda.

Albares yace a zahiri ne cewa akwai damuwa a kan ko al’ummar kasashen Turai zasu yarda da kafa runduna guda, amma kuma yace samun runduna guda ta fi tasiri a kan rundunoni har 27 dabam-dabam.

Wannan kira nasa yana zuwa kafin wani taron gaggawa da shugabannin Tarayyar Turai zasu yi ranar alhamis a Brussels domin maida martani bai daya ga barazanar shugaban Amurka Donald Trump na saye ko kwace yankin Greenland.

Wani kakakin majalisar TT ya tabbatar da cewa za a gudanar da wannan taron gaggawa na ranar alhamis duk da cewa shugaba Trump ya fada cewa shi da sakatare janar na NATO, Mark Rutte sun cimma daidaituwa kan yadda za a takali batun na Greenland.

Albares yace ba manufar wannan runduna da yake kiran da a kafa ce ta maye grbin NATO ba, amma kuma akwai bukatar nunawa duniya cewa ba wani wanda zai iya yi ma Turai barazanar soja ko ta tattalin arziki.

Wannan ra’ayi na kafa rundunar sojojin hadin guiwa ta kasashen Turai ba sabon abu ba ne. An fara gabatar da shi tun shekarar 1951 domin tunkarar tsohuwar Tarayyar Soviet da tabbatar da cewa ko kasar Jamus ta sake yin damara ba zata yi barazana ga makwabtanta ba. Majalisar dokokin kasar Faransa ita ce ta kashe wannan yunkurin ta hanyar jefa kuri’ar kin yarda da shi.

Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kungiyar Maharba Da ‘Yan Sintiri Sun Samu Kyautar Motoci
Next Post: Boko Haram Sun Farmaki Sansanin Sojoji A Borno

Karin Labarai Masu Alaka

Mutane 27 Sun Rasa Rayukan Su A Najeriya Afrika
Wasu Yara 50 Sun Kubuta Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai
Hotunan Hawan Sallah A Masarautar Bauchi Afrika
Ukraine Takai Hari Wajen Kera Makami Mai Linzami A Rasha Labarai
INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi Labarai
Tashoshin Mai Basa Iya Loda Mai A Rasha Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
  • Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba Najeriya
  • Gwamnatin Janhuriyar Nijar Ta Soke Lasisin Wasu Kamfanonin Dakon Mai Afrika
  • Thailand Da Cambodia Sun Fara Tattauunawa Kan Batun Tsagaita Wuta Labarai
  • Kimanin Mutane 200 Ne Suka A Mutu A Wani Harin Jirgin Yakin Sojin Najeriya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.