Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya Afrika

Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa
Published: January 22, 2026 at 7:45 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 22, 2026

A halin da ake ciki, Kasar Spain ta yi kira ga Tarayyar Turai da ta dauki matakan kirkiro rundunar sojojin hadin guiwa ta Kasashen Tarayyar Turai, domin ta zamo hannunka mai sanda ga duk wani mai neman nuna musu yatsa.

Ministan harkokin wajen Spain, Jose Manuel Albares ya fada ranar laraba cewa ya kamata kasashen Turai su fara da hada hancin kayan tsaron da suke da su da hade masana’antunsu na tsaro, kafin su kafa runduna guda.

Albares yace a zahiri ne cewa akwai damuwa a kan ko al’ummar kasashen Turai zasu yarda da kafa runduna guda, amma kuma yace samun runduna guda ta fi tasiri a kan rundunoni har 27 dabam-dabam.

Wannan kira nasa yana zuwa kafin wani taron gaggawa da shugabannin Tarayyar Turai zasu yi ranar alhamis a Brussels domin maida martani bai daya ga barazanar shugaban Amurka Donald Trump na saye ko kwace yankin Greenland.

Wani kakakin majalisar TT ya tabbatar da cewa za a gudanar da wannan taron gaggawa na ranar alhamis duk da cewa shugaba Trump ya fada cewa shi da sakatare janar na NATO, Mark Rutte sun cimma daidaituwa kan yadda za a takali batun na Greenland.

Albares yace ba manufar wannan runduna da yake kiran da a kafa ce ta maye grbin NATO ba, amma kuma akwai bukatar nunawa duniya cewa ba wani wanda zai iya yi ma Turai barazanar soja ko ta tattalin arziki.

Wannan ra’ayi na kafa rundunar sojojin hadin guiwa ta kasashen Turai ba sabon abu ba ne. An fara gabatar da shi tun shekarar 1951 domin tunkarar tsohuwar Tarayyar Soviet da tabbatar da cewa ko kasar Jamus ta sake yin damara ba zata yi barazana ga makwabtanta ba. Majalisar dokokin kasar Faransa ita ce ta kashe wannan yunkurin ta hanyar jefa kuri’ar kin yarda da shi.

Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kungiyar Maharba Da ‘Yan Sintiri Sun Samu Kyautar Motoci
Next Post: Boko Haram Sun Farmaki Sansanin Sojoji A Borno

Karin Labarai Masu Alaka

Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo Najeriya
Hari Da Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Mutane Da Dama A Darfur Labarai
Shugabannin Darikar Anglican Sun Bada Sanarwar Kafa Sabuwar Majalisa Afrika
Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu Afrika
An Kashe Falatsinawa Biyar A Wani Hari Da Isra’ila Takai Wata Makaranta A Gaza Tsaro
Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Jihar Filato Ta Sauke Hakimin Mushere Afrika
  • Shugaban Ukraine Ya Tattauna Da Trump Akan Zaman Lafiya Amurka
  • Gombe Ta Ƙaddamar da Allurar Rigakafin HIV Ta LEN PrEP Afrika
  • Fiye Da Fararen Hula 1000 Yunwa Ta Kashe A Sudan Afrika
  • Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika
  • Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.