Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa
Published: January 4, 2026 at 7:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 4, 2026

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, a matsayin magajin Malam Aminu Kano wajen kishin al’umma da jajircewa kan walwalar jihar Kano.

Tinubu ya bayyana hakan ne cikin wani saƙon taya murna da ya aike wa gwamnan bisa cika shekaru 63 da haihuwa.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Lahadi.

A cewar Shugaba Tinubu, sauƙin kai, tawali’u da kuma jajircewar Gwamna Abba Kabir Yusuf sun bayyana karara a yadda yake tafiyar da al’amuran mulki a jihar Kano.

Shugaban ƙasar ya ƙara da cewa yana da cikakken tabbaci cewa Gwamna Yusuf yana bin sahun hangen nesa da tafarkin Malam Aminu Kano wajen jagorancin jihar, wadda ke da muhimmiyar rawa a siyasar Arewacin Najeriya.

Tinubu ya ce jajircewar gwamnan wajen kare haƙƙin talakawan birni da na karkara na daga cikin manyan dalilan da ke tabbatar da hakan.

A cewarsa, shirye-shiryen sabunta birane da gwamnatin Kano ta ɓullo da su, musamman gina gadoji da tituna masu tsawon kilomita biyar biyar a kowace ƙaramar hukuma, sun nuna ƙwazon shugabancin gwamnan.

Haka kuma, Shugaba Tinubu ya yaba da ayyana dokar ta baci da Gwamna Yusuf ya yi a ɓangaren ilimi, inda ya ce hakan ya haifar da gagarumar ci gaba, musamman yadda ɗaliban jihar Kano suka samu sakamako mai kyau a jarabawar NECO.

A ƙarshe, Shugaba Tinubu ya yi wa Gwamna Abba Kabir Yusuf fatan tsawon rai da ƙarin shekaru na shugabanci masu albarka, tare da fatan ganin ƙarin ci gaba da bunƙasuwar jihar Kano.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Siyasa

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari
Next Post: Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela

Karin Labarai Masu Alaka

Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Farashin Mai A Kasuwannin Duniya Yayi ƙasa Kadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya Labarai
An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wike: Bazamuyi Sake Fubara Ya Sake Samun Nasara Ba Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Anyi Jefe-Jefe Yayin Rangadin Messi, A Indiya Wasanni
  • Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC Siyasa
  • Gangamin Wayar Da Kai Don Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Jihar Gombe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili Amurka
  • Rwanda Tana Keta Yarjejeniyar Zaman Lafiya – Tshisekedi Labarai
  • Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina Labarai
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.