Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa
Published: January 4, 2026 at 7:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 4, 2026

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, a matsayin magajin Malam Aminu Kano wajen kishin al’umma da jajircewa kan walwalar jihar Kano.

Tinubu ya bayyana hakan ne cikin wani saƙon taya murna da ya aike wa gwamnan bisa cika shekaru 63 da haihuwa.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Lahadi.

A cewar Shugaba Tinubu, sauƙin kai, tawali’u da kuma jajircewar Gwamna Abba Kabir Yusuf sun bayyana karara a yadda yake tafiyar da al’amuran mulki a jihar Kano.

Shugaban ƙasar ya ƙara da cewa yana da cikakken tabbaci cewa Gwamna Yusuf yana bin sahun hangen nesa da tafarkin Malam Aminu Kano wajen jagorancin jihar, wadda ke da muhimmiyar rawa a siyasar Arewacin Najeriya.

Tinubu ya ce jajircewar gwamnan wajen kare haƙƙin talakawan birni da na karkara na daga cikin manyan dalilan da ke tabbatar da hakan.

A cewarsa, shirye-shiryen sabunta birane da gwamnatin Kano ta ɓullo da su, musamman gina gadoji da tituna masu tsawon kilomita biyar biyar a kowace ƙaramar hukuma, sun nuna ƙwazon shugabancin gwamnan.

Haka kuma, Shugaba Tinubu ya yaba da ayyana dokar ta baci da Gwamna Yusuf ya yi a ɓangaren ilimi, inda ya ce hakan ya haifar da gagarumar ci gaba, musamman yadda ɗaliban jihar Kano suka samu sakamako mai kyau a jarabawar NECO.

A ƙarshe, Shugaba Tinubu ya yi wa Gwamna Abba Kabir Yusuf fatan tsawon rai da ƙarin shekaru na shugabanci masu albarka, tare da fatan ganin ƙarin ci gaba da bunƙasuwar jihar Kano.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Siyasa

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari
Next Post: Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela

Karin Labarai Masu Alaka

Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kwankwaso: Gwamnatin Kano Tamuce Baki Daya, Tafiya APC Allah Ya Raka Taki Gona! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5 Labarai
  • Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika
  • An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
  • Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar Afrika
  • Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni
  • Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
  • Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot. Wasanni
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.