Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnan Jihar Kano Ya Fice Daga Jam’iyar NNPP
Published: January 23, 2026 at 4:16 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP), yana mai danganta matakin da tsanantar rikice-rikicen cikin gida a jam’iyyar da kuma buƙatar kare muradun al’ummar jihar Kano gaba ɗaya.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Juma’a.

A cikin wasiƙar da ya aike wa Shugaban mazabar Diso-Chiranchi na jam’iyyar NNPP a Ƙaramar Hukumar Gwale, gwamnan ya sanar da janyewarsa daga jam’iyyar, wanda zai fara aiki daga ranar Juma’a, 23 ga Janairu, 2026.

“Ina rubuta wannan wasiƙa cikin matuƙar godiya domin sanar da shugabannin jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) cewa na yanke shawarar ajiye kasancewata ɗan jam’iyyar, daga ranar Juma’a, 23 ga Janairu, 2026.”

Gwamna Yusuf ya bayyana godiyarsa ga jam’iyyar bisa damar da ta ba shi da kuma goyon bayan da ya samu tun farkon tafiyarsa ta siyasa a ƙarƙashin NNPP.

Ya kuma yi nuni da cewa jam’iyyar na fuskantar rikice-rikice na cikin gida da kuma ƙalubalen shari’a da suka daɗe suna dagula tsarinta a matakin ƙasa.

A cewarsa, rikice-rikicen sun haifar da rarrabuwar kawuna tare da raunana haɗin kan jam’iyyar.

Gwamnan ya ce ya ɗauki matakin ne bayan zurfin nazari, kuma bisa la’akari da muradun jama’a kawai.

Ya jaddada cewa ya ɗauki wannan mataki ne cikin kyakkyawar niyya ba tare da wata ƙiyayya ba.

“Na ɗauki wannan mataki cikin kyakkyawar niyya, ba tare da wata muguwar manufa ko ƙiyayya ba, tare da ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban jihar Kano.”

Gwamnan ya fice tare da mambobi 21 na Majalisar Dokokin jihar Kano, mambobi 8 na Majalisar Wakilai ta Tarayya, da kuma shugabannin ƙananan hukumomi 44 na Jihar Kano.

Sakataren jam’iyyar NNPP na Ward ɗin Diso-Chiranchi, Kabiru Zubairu, ya tabbatar da karɓar wasiƙar tare da yabawa gwamnan bisa ayyukan ci gaba da ya aiwatar a fannoni daban-daban.

Siyasa

Post navigation

Previous Post: Tsohon Lauyan Amurka Jack Smith Ya Fadi Maganganu Game Da Donald Trump
Next Post: Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamna Abba Ya Gana Da Kwankwaso Kamun Ganawarsa Da Tinubu Siyasa
Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba Labarai
Majalisun Najeriya Sun Amince Ta Karin Kasafin Kudi Afrika
Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya
Kasashen Yankin Gulf Sun Bukaci Amurka Takawo Karshen Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana Afrika
  • Farmakin Da Aka Kai Makarantar Mata A Iran Yayi Ajalin Yara Da Dama Afrika
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe  Afrika
  • RSF Ta Kasar Sudan, Tana Yin Garkuwa Da Mazauna A Yankin Darfur Afrika
  • An Yankewa Prime Ministan Kasar Tunisiya Hukuncin Shekaru 24 A Gidan Yari Afrika
  • Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
  • Kasar Morocco Ta Kwashe ‘Yan Kasar Daga Sassan Ambaliyar Ruwa Afrika
  • An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.